• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ta Shirya Bikin CIIE?

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Kasar Sin Ta Shirya Bikin CIIE?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan nan, an shirya bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin daga ketare, wato CIIE a takaice, karo na 7 a birnin Shanghai na Sin, inda kasar Najeriya ta nuna boyayyen karfinta a fannin cinikayya.

 

Shugabar kwamitin inganta aikin fitar da kayayyaki ta kasar Najeriya Nonye Ayeni ce ta jagoranci tawagar Najeriya wajen halartar bikin CIIE na wannan karo, inda suka nuna dimbin kayayyakin kasar Najeriya, irinsu amfanin gona, da ma’adinai, da dai sauransu. Kana a yayin da take hira da abokin aikina Murtala Zhang, Malama Ayeni ta ce, yadda kasar Sin ta yarda da shigowar gyada daga Najeriya cikin kasuwannin Sin zai amfani manoma da ‘yan kasuwa na Najeriya. Tana kuma fatan yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, don neman sayar da karin kayayyakin Najeriya zuwa ketare.

  • Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti
  • Shugabannin Sin Da Italiya Sun Kalli Kayayyakin Tarihi Da Aka Dawo Da Su Kasar Sin

Ban da Najeriya, sauran kasashen Afirka da suka nemi damammaki a wajen bikin CIIE na bana sun hada da Benin, da Madagascar, da Namibia, da dai sauransu. A bikin CIIE na bara, Abarba ta kasar Benin ta samu karbuwa sosai, har ma an kulla kwangilolin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 60. Ganin wannan misali ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka suka halarci bikin CIIE na wannan karo, tare da kayayyakinsu, irinsu ruwan zuma, da naman rago, da kashu, da dai makamantansu.

 

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

Tun daga watan Satunban bana, kasar Sin ta sanar da yafewa kayayyakin kasashe marasa karfin tattalin arziki, ciki har da kasashe 33 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Kana a wani ci gaba, kasar Sin ta kara fadin yankin baje kolin kayayyakin kasashen Afirka, a bikin CIIE na wannan karo, da samar da rumfunan baje koli fiye da 120 kyauta ga kasashe 37 marasa karfin tattalin arziki. Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin ke kokarin taimakon kasashen Afirka, wajen fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin, da halartar tsarin samar da kayayyakin na duniya.

 

Hakika, da ma an tsara bikin CIIE din ne domin taimakawa sauran kasashe samun damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin kasar Sin, wanda ya kasance irinsa na farko a duniya. Sai dai watakila, wani ya yi tambaya game da ko mene ne dalilin da ya sa kasar Sin ta shirya bikin? kuma me ya sa take taimakon sauran kasashe da damar sayar da kayayyakin su, tare da neman riba a kasuwannin Sin?

 

To, dalili na farko shi ne manufar kasar Sin ta tabbatar da cin moriyar juna, yayin da take hadin gwiwa da wata kasa ta daban. Idan mun dauki hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin ciniki a matsayin misali, za mu ga yadda kasar Sin ke kokarin neman samun daidaito a fannin cinikin da ake yi tsakanin bangarorin 2, inda ta saukaka aikin fitar da kayayyakin abinci na Afirka zuwa kasar Sin, da sanya karin kamfanonin Afirka amfani da dandalin kasuwanci na yanar gizo na kasar Sin wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar.

 

Ban da haka, wani dalili na daban shi ne manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje. Ta hanyar kara bude kofarta ga ketare, kasar Sin ta zama babbar abokiyar huldar ciniki ta kasashe da yankuna fiye da 150, cikin shekaru gwammai da suka gabata, inda ta kasance kan gaba a duniya, a fannonin yawan hajojin da take cinikinsu, da yawan jarin da take janyowa daga ketare, da wanda take zuba wa sauran kasashe. Wadannan nasarori sun shaida amfanin manufarta ta bude kofa, a fannonin raya kai, gami da haifar da moriya ga dukkanin kasashen duniya. Kuma dole ne kasar ta dauki karin matakai na bude kofa, don samar da damammaki na samun ci gaban bai daya a duniya, don kawar da mummunan tasirin da wasu matakan radin kai da wasu kasashe suka dauka suka haifar.

 

A karshe, tabbatar da cin moriyar juna, ko bude kofa, dukkansu na da alaka da babbar manufar kasar ta gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. A ganin Sinawa, don cimma burin tabbatarwa daukacin dan Adam da ci gaba mai dorewa, abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da nasarar kowa, a maimakon sanya wani bangare shi kadai cin nasara. Ya kamata al’ummun kasashe daban daban su yi kokarin musayar ra’ayi da hadin kai, don neman kawar da rikici, da tabbtar da moriyar dukkan bangarori cikin daidaito, gami da samun ci gaba na bai daya a hadin gwiwarsu. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti

Next Post

Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Related

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

2 weeks ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

3 weeks ago
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu
Ra'ayi Riga

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

3 weeks ago
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye
Ra'ayi Riga

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

4 weeks ago
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

2 months ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

2 months ago
Next Post
Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.