ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

by Sulaiman
11 months ago
vector illustration of Nigeria flag and map

vector illustration of Nigeria flag and map

Kusan za a iya cewa, shekaru 65 na samun ‘yancin kan Nijeriya, sun kai munzalin a ce yaro ya girma ya kuma waye.

 

Sai dai, Nijeriya wadda ta yi bikin cika sheka 65 da samun’yancin kan a makon da ya gabata, wannan batun bai kasance hakan ba, musamman saboda da gadawar cika alkawura daga bangaren mahukunta tun a baya, har kumar zuwa yau.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
  • ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

A nan za a iya cewa, wannan batun, ya faro ne tun daga lokacin Jamhuriya ta farko wato lokacin tsohon mulkin marigayi Nnamdi Azikiwe, inda kuma lamarun juyin mulkin soji suka kutso ciki wanda kuma matsalar yakin basasa da ya barke a kasar, ya kara dagula al’amura.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

Kazalika, tarihin Dimokiradiyyar kasar ya sha cin karo da kwam gaba kwam baya kusan za a iya cewa, tun bayan dawowar mulkin Demokaradiyya a 1979 da kuma sake dora kasar a wata turbar ta Demokiradiyyar a 1999.

 

Alal misali, jamhuriyya ta hudu ta kasance ta jima sosai, amma kusan babu wasu ayyukan na inganta rayuwar ‘yan kasar da za a bigi Kirji a ce gasu an gani a kasar a zahiri.

 

Idan aka dubi bangaren samar da hasken wutar lantarki kusan za a iya cewa, karni da dama da suka bace, har zuwa yau Nijeriya ta gaza samar da karfin wutar da kuma rabar da ita da ta kai karfin Megawatts 5,000 musamman duba da cewa, wannan adadin bai wuce na wani can karamin birini ne, za a samar ba, idan aka yi la’kari da kasar, wadda ake mata kirari da uwa ga daukacin kasahen da ke a nahiyar Afirka.

 

Bugu da kari, an jibga dimbin biliyoyin Naira domin farfado da fannin, amma har zuwa yau, haka ba ta comma ruwa ba.

 

Wani karin abin takaicin shi ne, na kalubalen rashin tsaro da ya ke ci gaba da wata zama babbar barazana ga kasar, domin sama da rayukan ‘yan kasar 169,000 da ba su ji ba su kuma gani ba aka hallaka daga tsakanin 2006 zuwa 2021.

 

Sun rasa rayukansu ne, ko dai, sanadiyyar wasu tashe-tashen hankula ko na hare-haren Boko Haram ko na ‘yan bindiga daji ko a rikice-rikicen manoma da Fulani Makiyaya ko kuma a rikice-rikicen kabilanci.

 

A takaice, za a iya cewa, dubban mutane ne, suka rasa rayukansu kusan a karni biyu da suka bace, inda adadin ya rubanya na wadanda aka hallaka, a lokacin yakin basasa a kasar.

 

Hakazalika, a bangaren batun gudanar da sauye-sauye tare da yin amfani da fasahar zamani a harkar gudanar da zabe a kasar, musamman domin a gudanar da sahihin zabe da kuma dakile matsalar sayen kuri’u, amma har zuwa yau, babu abinda ya sauya wanda daga karshe, ‘yan takardar da aka yiwa wa kaci ka tashi a lokacin da aka tabka magudi a zabubbukan, ke garzaywa zuwa kotu, domin bin hakwinsu.

 

Kazalika, batun cin hanci da rashawa na daya daga cikin matsalar da ta daidaita kasar, an yi kiyasin cewa, a 2012, Nijeriya ta tabka asarar da ta kai ta sama da dala biliyan 400.

 

Wannan adadin sun isa ace, an yi amfani da su, wajen gina hanyotin Layin Dogo da makarantu da gina Asibiti da kuma masana’antu, amma abin bakin ciki, wasu sun yi kwaciyar Magirbi kan wadannan kudaden.

 

Amma duk da wadannan matsalolin, an gudanar da bikin na samun ‘ yancin kan kasar, musamman a yayin da, ake ci gaba da nuna damuwa a kasar .

A bangaren masana’antar kirkire-kirkiren fasaha, fannin ya samu daukaka har a idon duniya, inda misali, fitattun mawaka da kuma a bangaren masu shiyar Fina-Finai, a masana’antar Nollywood suka kai wani mataki a duniya, musamman wajrn birge masu bibiyarsu.

Alal misali, daga mawaki irinsu Dabido, Wizkid, Burna Boy, har ta kai ga, sun shahara a Nahiyar Turai.

Haka batun dai yake a fannin kimiyyar zamani na kasar, duba da cewa, Nijeriya ta kai matakin mamaye kasashen da ke Afirka a bangaren zuba kudade, a fannin.

Suma matasan ‘yan kasuwa, musamman a jihar Legas da kuma Abuja, inda suke kirirar manhajar zamani, ta hada-hadar kudade da da kuma samar da kayan fasahar zamani.

Karin wata matsalar da ke ci gaba da zamowa ruwan dare a kasar shi ne, na yawan samun karuwar kwararrun Likitoci, da ke ficewa zuwa kasashen duniya, domin neman aikin, ganin cewa, a kasashen ana tsoka, inda a Birtaniya suke ci gaba baza hajarsu, su kuma kwararrun Injinoyi na kasar nan nan da suka noma zuwa Amurka, ke ci gaba da zan akalar tsari na fannin na kasar.

Duk hakan na akuwa ne, saboda gazawar tsarin kasar wanda hakan ya sanya, aka gaza ci gaba rike irin wadannan zakakuran da ake da su a kasar.

Nigeriya ta kasance, ta na alumma sama da kaso 60, wanda kuma masu shekaru 25, suka kasance masu hazakar da za a iya amfani da ita wajen ciyar da kasar gaba.

Bugu da kari, kasar na kuma da dimbin marasa aikin yi wanda hakan ya kara haifar da samun aikata nau’ukan laifuka da dama.

Hakazalika, akwai da dama da suka haura har zuwa iyakokin kasar, misali ta hanyar amfani da kungiyar ECOWAS da kuma yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci ta Afirka wato AfCFTA wanda hakan ya bai wa kasar damar wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikinta.

Amma saboda rashin tafiyar da shugabanci yadda ya kamata da rashin ingantattun kayan aiki da rashin samar da kyakyawan yanayi a bangaren harkar tsaro, wadannan matsalolin, suna kasar cin gajiyar wannan damar.

Kasar ta cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai, amma tana ci gaba da fuskantar kalubale iri-iri da suka hada da cin hanci da rashawa, matsalar rashin tsaro da ta hana yara ci gaba da zuba makaranta.

A nan, zamu iya cewa shekaru 65, sun isa ace an koyi darasi a kasar.

Kazalika, ra’ayinmu a nan shi ne, abinda ake bukata a bangaren masu rike da madafun iko, su mayar da hankali wajen wandar da tsare-tsaren da za su inganta rayuwar ‘yan kasar da kuma ciyar da kasar gaba.

Yancin kai
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Yancin kai
Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG
Ra'ayinmu

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

July 31, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Next Post
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.