• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ta Shirya Bikin CIIE?

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Kasar Sin Ta Shirya Bikin CIIE?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan nan, an shirya bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin daga ketare, wato CIIE a takaice, karo na 7 a birnin Shanghai na Sin, inda kasar Najeriya ta nuna boyayyen karfinta a fannin cinikayya.

 

Shugabar kwamitin inganta aikin fitar da kayayyaki ta kasar Najeriya Nonye Ayeni ce ta jagoranci tawagar Najeriya wajen halartar bikin CIIE na wannan karo, inda suka nuna dimbin kayayyakin kasar Najeriya, irinsu amfanin gona, da ma’adinai, da dai sauransu. Kana a yayin da take hira da abokin aikina Murtala Zhang, Malama Ayeni ta ce, yadda kasar Sin ta yarda da shigowar gyada daga Najeriya cikin kasuwannin Sin zai amfani manoma da ‘yan kasuwa na Najeriya. Tana kuma fatan yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, don neman sayar da karin kayayyakin Najeriya zuwa ketare.

  • Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti
  • Shugabannin Sin Da Italiya Sun Kalli Kayayyakin Tarihi Da Aka Dawo Da Su Kasar Sin

Ban da Najeriya, sauran kasashen Afirka da suka nemi damammaki a wajen bikin CIIE na bana sun hada da Benin, da Madagascar, da Namibia, da dai sauransu. A bikin CIIE na bara, Abarba ta kasar Benin ta samu karbuwa sosai, har ma an kulla kwangilolin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 60. Ganin wannan misali ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka suka halarci bikin CIIE na wannan karo, tare da kayayyakinsu, irinsu ruwan zuma, da naman rago, da kashu, da dai makamantansu.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Tun daga watan Satunban bana, kasar Sin ta sanar da yafewa kayayyakin kasashe marasa karfin tattalin arziki, ciki har da kasashe 33 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Kana a wani ci gaba, kasar Sin ta kara fadin yankin baje kolin kayayyakin kasashen Afirka, a bikin CIIE na wannan karo, da samar da rumfunan baje koli fiye da 120 kyauta ga kasashe 37 marasa karfin tattalin arziki. Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin ke kokarin taimakon kasashen Afirka, wajen fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin, da halartar tsarin samar da kayayyakin na duniya.

 

Hakika, da ma an tsara bikin CIIE din ne domin taimakawa sauran kasashe samun damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin kasar Sin, wanda ya kasance irinsa na farko a duniya. Sai dai watakila, wani ya yi tambaya game da ko mene ne dalilin da ya sa kasar Sin ta shirya bikin? kuma me ya sa take taimakon sauran kasashe da damar sayar da kayayyakin su, tare da neman riba a kasuwannin Sin?

 

To, dalili na farko shi ne manufar kasar Sin ta tabbatar da cin moriyar juna, yayin da take hadin gwiwa da wata kasa ta daban. Idan mun dauki hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin ciniki a matsayin misali, za mu ga yadda kasar Sin ke kokarin neman samun daidaito a fannin cinikin da ake yi tsakanin bangarorin 2, inda ta saukaka aikin fitar da kayayyakin abinci na Afirka zuwa kasar Sin, da sanya karin kamfanonin Afirka amfani da dandalin kasuwanci na yanar gizo na kasar Sin wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar.

 

Ban da haka, wani dalili na daban shi ne manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje. Ta hanyar kara bude kofarta ga ketare, kasar Sin ta zama babbar abokiyar huldar ciniki ta kasashe da yankuna fiye da 150, cikin shekaru gwammai da suka gabata, inda ta kasance kan gaba a duniya, a fannonin yawan hajojin da take cinikinsu, da yawan jarin da take janyowa daga ketare, da wanda take zuba wa sauran kasashe. Wadannan nasarori sun shaida amfanin manufarta ta bude kofa, a fannonin raya kai, gami da haifar da moriya ga dukkanin kasashen duniya. Kuma dole ne kasar ta dauki karin matakai na bude kofa, don samar da damammaki na samun ci gaban bai daya a duniya, don kawar da mummunan tasirin da wasu matakan radin kai da wasu kasashe suka dauka suka haifar.

 

A karshe, tabbatar da cin moriyar juna, ko bude kofa, dukkansu na da alaka da babbar manufar kasar ta gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. A ganin Sinawa, don cimma burin tabbatarwa daukacin dan Adam da ci gaba mai dorewa, abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da nasarar kowa, a maimakon sanya wani bangare shi kadai cin nasara. Ya kamata al’ummun kasashe daban daban su yi kokarin musayar ra’ayi da hadin kai, don neman kawar da rikici, da tabbtar da moriyar dukkan bangarori cikin daidaito, gami da samun ci gaba na bai daya a hadin gwiwarsu. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti

Next Post

Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Related

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi
Ra'ayi Riga

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

2 days ago
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 
Ra'ayi Riga

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

5 days ago
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
Ra'ayinmu

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

2 weeks ago
Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
Ra'ayinmu

Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba

3 weeks ago
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara
Ra'ayinmu

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

3 weeks ago
Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

2 months ago
Next Post
Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.