ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ta Shirya Bikin CIIE?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
CIIE

Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan nan, an shirya bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin daga ketare, wato CIIE a takaice, karo na 7 a birnin Shanghai na Sin, inda kasar Najeriya ta nuna boyayyen karfinta a fannin cinikayya.

 

Shugabar kwamitin inganta aikin fitar da kayayyaki ta kasar Najeriya Nonye Ayeni ce ta jagoranci tawagar Najeriya wajen halartar bikin CIIE na wannan karo, inda suka nuna dimbin kayayyakin kasar Najeriya, irinsu amfanin gona, da ma’adinai, da dai sauransu. Kana a yayin da take hira da abokin aikina Murtala Zhang, Malama Ayeni ta ce, yadda kasar Sin ta yarda da shigowar gyada daga Najeriya cikin kasuwannin Sin zai amfani manoma da ‘yan kasuwa na Najeriya. Tana kuma fatan yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, don neman sayar da karin kayayyakin Najeriya zuwa ketare.

ADVERTISEMENT
  • Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti
  • Shugabannin Sin Da Italiya Sun Kalli Kayayyakin Tarihi Da Aka Dawo Da Su Kasar Sin

Ban da Najeriya, sauran kasashen Afirka da suka nemi damammaki a wajen bikin CIIE na bana sun hada da Benin, da Madagascar, da Namibia, da dai sauransu. A bikin CIIE na bara, Abarba ta kasar Benin ta samu karbuwa sosai, har ma an kulla kwangilolin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 60. Ganin wannan misali ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka suka halarci bikin CIIE na wannan karo, tare da kayayyakinsu, irinsu ruwan zuma, da naman rago, da kashu, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Tun daga watan Satunban bana, kasar Sin ta sanar da yafewa kayayyakin kasashe marasa karfin tattalin arziki, ciki har da kasashe 33 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Kana a wani ci gaba, kasar Sin ta kara fadin yankin baje kolin kayayyakin kasashen Afirka, a bikin CIIE na wannan karo, da samar da rumfunan baje koli fiye da 120 kyauta ga kasashe 37 marasa karfin tattalin arziki. Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin ke kokarin taimakon kasashen Afirka, wajen fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin, da halartar tsarin samar da kayayyakin na duniya.

 

Hakika, da ma an tsara bikin CIIE din ne domin taimakawa sauran kasashe samun damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin kasar Sin, wanda ya kasance irinsa na farko a duniya. Sai dai watakila, wani ya yi tambaya game da ko mene ne dalilin da ya sa kasar Sin ta shirya bikin? kuma me ya sa take taimakon sauran kasashe da damar sayar da kayayyakin su, tare da neman riba a kasuwannin Sin?

 

To, dalili na farko shi ne manufar kasar Sin ta tabbatar da cin moriyar juna, yayin da take hadin gwiwa da wata kasa ta daban. Idan mun dauki hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin ciniki a matsayin misali, za mu ga yadda kasar Sin ke kokarin neman samun daidaito a fannin cinikin da ake yi tsakanin bangarorin 2, inda ta saukaka aikin fitar da kayayyakin abinci na Afirka zuwa kasar Sin, da sanya karin kamfanonin Afirka amfani da dandalin kasuwanci na yanar gizo na kasar Sin wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar.

 

Ban da haka, wani dalili na daban shi ne manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje. Ta hanyar kara bude kofarta ga ketare, kasar Sin ta zama babbar abokiyar huldar ciniki ta kasashe da yankuna fiye da 150, cikin shekaru gwammai da suka gabata, inda ta kasance kan gaba a duniya, a fannonin yawan hajojin da take cinikinsu, da yawan jarin da take janyowa daga ketare, da wanda take zuba wa sauran kasashe. Wadannan nasarori sun shaida amfanin manufarta ta bude kofa, a fannonin raya kai, gami da haifar da moriya ga dukkanin kasashen duniya. Kuma dole ne kasar ta dauki karin matakai na bude kofa, don samar da damammaki na samun ci gaban bai daya a duniya, don kawar da mummunan tasirin da wasu matakan radin kai da wasu kasashe suka dauka suka haifar.

 

A karshe, tabbatar da cin moriyar juna, ko bude kofa, dukkansu na da alaka da babbar manufar kasar ta gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. A ganin Sinawa, don cimma burin tabbatarwa daukacin dan Adam da ci gaba mai dorewa, abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da nasarar kowa, a maimakon sanya wani bangare shi kadai cin nasara. Ya kamata al’ummun kasashe daban daban su yi kokarin musayar ra’ayi da hadin kai, don neman kawar da rikici, da tabbtar da moriyar dukkan bangarori cikin daidaito, gami da samun ci gaba na bai daya a hadin gwiwarsu. (Bello Wang)

CIIE
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
CIIE
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa
Ra'ayi Riga

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

June 15, 2026
Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Next Post
Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.