ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Kasar Sin Ta Shirya Bikin CIIE?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
CIIE

Daga ranar 5 zuwa ta 10 ga watan nan, an shirya bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin daga ketare, wato CIIE a takaice, karo na 7 a birnin Shanghai na Sin, inda kasar Najeriya ta nuna boyayyen karfinta a fannin cinikayya.

 

Shugabar kwamitin inganta aikin fitar da kayayyaki ta kasar Najeriya Nonye Ayeni ce ta jagoranci tawagar Najeriya wajen halartar bikin CIIE na wannan karo, inda suka nuna dimbin kayayyakin kasar Najeriya, irinsu amfanin gona, da ma’adinai, da dai sauransu. Kana a yayin da take hira da abokin aikina Murtala Zhang, Malama Ayeni ta ce, yadda kasar Sin ta yarda da shigowar gyada daga Najeriya cikin kasuwannin Sin zai amfani manoma da ‘yan kasuwa na Najeriya. Tana kuma fatan yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar, don neman sayar da karin kayayyakin Najeriya zuwa ketare.

ADVERTISEMENT
  • Ya Kamata A Dakatar Da Duk Wasu Wasanni A Sifaniya Saboda Ambaliyar Balencia – Ancelotti
  • Shugabannin Sin Da Italiya Sun Kalli Kayayyakin Tarihi Da Aka Dawo Da Su Kasar Sin

Ban da Najeriya, sauran kasashen Afirka da suka nemi damammaki a wajen bikin CIIE na bana sun hada da Benin, da Madagascar, da Namibia, da dai sauransu. A bikin CIIE na bara, Abarba ta kasar Benin ta samu karbuwa sosai, har ma an kulla kwangilolin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 60. Ganin wannan misali ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka suka halarci bikin CIIE na wannan karo, tare da kayayyakinsu, irinsu ruwan zuma, da naman rago, da kashu, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Tun daga watan Satunban bana, kasar Sin ta sanar da yafewa kayayyakin kasashe marasa karfin tattalin arziki, ciki har da kasashe 33 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Kana a wani ci gaba, kasar Sin ta kara fadin yankin baje kolin kayayyakin kasashen Afirka, a bikin CIIE na wannan karo, da samar da rumfunan baje koli fiye da 120 kyauta ga kasashe 37 marasa karfin tattalin arziki. Wadannan matakai sun nuna yadda kasar Sin ke kokarin taimakon kasashen Afirka, wajen fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin, da halartar tsarin samar da kayayyakin na duniya.

 

Hakika, da ma an tsara bikin CIIE din ne domin taimakawa sauran kasashe samun damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasuwannin kasar Sin, wanda ya kasance irinsa na farko a duniya. Sai dai watakila, wani ya yi tambaya game da ko mene ne dalilin da ya sa kasar Sin ta shirya bikin? kuma me ya sa take taimakon sauran kasashe da damar sayar da kayayyakin su, tare da neman riba a kasuwannin Sin?

 

To, dalili na farko shi ne manufar kasar Sin ta tabbatar da cin moriyar juna, yayin da take hadin gwiwa da wata kasa ta daban. Idan mun dauki hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin ciniki a matsayin misali, za mu ga yadda kasar Sin ke kokarin neman samun daidaito a fannin cinikin da ake yi tsakanin bangarorin 2, inda ta saukaka aikin fitar da kayayyakin abinci na Afirka zuwa kasar Sin, da sanya karin kamfanonin Afirka amfani da dandalin kasuwanci na yanar gizo na kasar Sin wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar.

 

Ban da haka, wani dalili na daban shi ne manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje. Ta hanyar kara bude kofarta ga ketare, kasar Sin ta zama babbar abokiyar huldar ciniki ta kasashe da yankuna fiye da 150, cikin shekaru gwammai da suka gabata, inda ta kasance kan gaba a duniya, a fannonin yawan hajojin da take cinikinsu, da yawan jarin da take janyowa daga ketare, da wanda take zuba wa sauran kasashe. Wadannan nasarori sun shaida amfanin manufarta ta bude kofa, a fannonin raya kai, gami da haifar da moriya ga dukkanin kasashen duniya. Kuma dole ne kasar ta dauki karin matakai na bude kofa, don samar da damammaki na samun ci gaban bai daya a duniya, don kawar da mummunan tasirin da wasu matakan radin kai da wasu kasashe suka dauka suka haifar.

 

A karshe, tabbatar da cin moriyar juna, ko bude kofa, dukkansu na da alaka da babbar manufar kasar ta gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. A ganin Sinawa, don cimma burin tabbatarwa daukacin dan Adam da ci gaba mai dorewa, abin da ya fi muhimmanci shi ne tabbatar da nasarar kowa, a maimakon sanya wani bangare shi kadai cin nasara. Ya kamata al’ummun kasashe daban daban su yi kokarin musayar ra’ayi da hadin kai, don neman kawar da rikici, da tabbtar da moriyar dukkan bangarori cikin daidaito, gami da samun ci gaba na bai daya a hadin gwiwarsu. (Bello Wang)

CIIE
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
CIIE
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba – Atiku

Okawa Bai Taimake Ni Da Kuɗin Jihar Delta Don Na Yi Kamfe A 2023 Ba - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.