• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa “TikTok Refugee” Na Amurka Suke Ta Kama REDnote Ta Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa “TikTok Refugee” Na Amurka Suke Ta Kama REDnote Ta Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

REDnote wata manhajar sada zumunta ce da ke samun karbuwa a kasar Sin, kuma ni kaina ina bibiyar shafukan REDnote. Sai dai a kwanakin nan, na tarar da dimbin masu bibiyar shafin TikTok da suka fito daga kasar Amurka, wadanda suke kiran kansu “TikTok Refugee”, wadanda ke ta kaura zuwa REDnote, kuma a cewarsu, dalilin hakan shi ne don tinkarar matsalar haramcin da gwamnatin kasar Amurka ka iya sanya wa TikTok.

Lallai a baya, gwamnatin kasar Amurka ta fake da sunan wai “tsaron kasa”, kuma ta bukaci kamfanin Bytedance da ke mallakar TikTok, da ya sayar da TikTok din ga bangaren Amurka kafin ranar 19 ga watan shekarar 2025, in ba haka ba, za ta haramta yin amfani da manhajar a fadin kasar. Sai dai ba a yi zaton hakan ya sa dimbin masu bibiyar shafukan TikTok na kasar ta Amurka za su kama REDnote, a maimakon zabar manhajojin sada zumunta ta cikin gida ba. A game da hakan, wasu daga cikinsu sun ce, dalili shi ne don nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin Amurka ta yi.

  • Ma’aikatar Wajen Sin: Yamadidin Da Ake Yi Na “An Tilasta Wa Mutane Yin Aikin Dole” Karya Ne
  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka

Aria Lynn Grayson, mai bibiyar shafin TikTok ce daga Los Angeles, wadda ta kan samar da hotunan bidiyo game da ilmin kwalliya. A hoton bidiyon da ta bayar a shafinta na REDnote, ta ce, “Gwamnatin kasarmu tana yunkurin haramta yin amfani da TikTok, wai manhajar tana barazana ga tsaron kasa, kuma wai kasar Sin na neman satar bayananmu, amma a hakika kasancewar mu masu ziyartar shafukan yanar gizo, musamman na shafukan TikTok, mun san abubuwan da ke faruwa a duniya.” Sai kuma wata mai bibiyar shafin TikTok da ake kira Amy daga jihar Massachusetts, tana ganin cewa, kasar Sin ba ta sha’awar sanin “me mu ka fi son ci”. Ta ce, “A hakika, gwamnatin kasar Amurka ita ce take sa ido a kan al’ummarta da satar bayananmu.” Ta kara da cewa, aminanta da yawa na TikTok sun sadu da juna a shafin REDnote, “Ina matukar jin dadin yin musaya tare da ‘yan Amurka masu bibiyar TikTok da suka kaura zuwa nan, a ganina tamkar juyin juya hali ne muka yi. Muna jin dadin yin musuyar ra’ayoyi tare da mutanen kasar Sin ta dandalin, duk da kasancewar bambancin al’adu a tsakaninmu.”

“Barkanku dai, mutanen kasar Sin, ni dan kasar Amurka ne, idan kuna bukatar taimako wajen koyon Turancin Ingilishi, to, ina nan!” “Barkanmu dai! Ni mai nazarin halittun teku ne daga jihar California, kuma zan so in samu abokai a nan, kuma ina son koyon Sinanci, kuma zan iya taimaka muku koyon Turancin Ingilishi!” “Ko za ku iya nuna min titunan kasar Sin?”…

Kamar yadda Amy ta fada, dimbin masu bibiyar shafin TikTok sun yi musaya sosai tare da masu bibbiyar shafin REDnote, bayan da suka sauke manhajar, inda suke yin amfani da Turanci ko kuma Sinancin da tamkar suka fassara da wata nau’in manhaja, suna nuna harkokin da suka shafi rayuwarsu ta yau da kullum. Kuma masu bibiyar shafin REDnote na kasar Sin ma sun yi musaya sosai tare da su. Akwai kuma wani dan Amurka da ya samu sakwannin fatan alheri kusan dubu biyar daga Sinawa masu bibiyar shafin REDnote, sa’o’i kadan bayan da ya bayyana fatan samun gaisuwar fatan alheri daga mutanen kasar Sin a shafinsa na REDnote a ranar haihuwarsa.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

“A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka a tsakanin Sin da Amurka, an sada sabuwar zumunta a tsakanin kasashen biyu ta wata manhajar da a baya mutanen kasashen waje ba sa amfani da ita sosai.” In ji jaridar Wallstreet Journal. A duk lokacin da take da fifiko a fannin fasahohi, ta kan tabo maganar ‘yancin tattalin arziki, a lokacin da ba ta da shi kuma, sai ta jaddada muhimmancin “tsaron kasa”, wannan mataki ne da gwamnatin kasar Amurka ta saba dauka. Sai dai a wannan karo, al’ummar kasar ba su yarda a kwace hakkinsu ba.

Yau kimanin shekaru 54 da suka gabata, ta diplomasiyyar wasan kwallon tebur, kasashen Sin da Amurka suka bude kofar yin cudanya da juna, tare da farfado da huldarsu, matakin da ya haifar da muhimmin tasiri ga yanayin duniya. Bayan tsawon shekaru 54, a lokacin da huldar kasashen biyu ke kara fuskantar kalubale, muna fatan dandalin REDnote zai zamanto tamkar sabuwar hanyar da za ta kara fahimtar da al’ummar kasar Amurka game da hakikanin yanayin da ake ciki a kasar Sin, da karfafa cudanya a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za a farfado da huldar kasashen biyu, don kwantar da hankulan al’ummar kasashen biyu da na duniya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Next Post

Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

19 hours ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

21 hours ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

3 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

4 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

4 days ago
Next Post
Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.