ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa “TikTok Refugee” Na Amurka Suke Ta Kama REDnote Ta Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
TikTok

REDnote wata manhajar sada zumunta ce da ke samun karbuwa a kasar Sin, kuma ni kaina ina bibiyar shafukan REDnote. Sai dai a kwanakin nan, na tarar da dimbin masu bibiyar shafin TikTok da suka fito daga kasar Amurka, wadanda suke kiran kansu “TikTok Refugee”, wadanda ke ta kaura zuwa REDnote, kuma a cewarsu, dalilin hakan shi ne don tinkarar matsalar haramcin da gwamnatin kasar Amurka ka iya sanya wa TikTok.

Lallai a baya, gwamnatin kasar Amurka ta fake da sunan wai “tsaron kasa”, kuma ta bukaci kamfanin Bytedance da ke mallakar TikTok, da ya sayar da TikTok din ga bangaren Amurka kafin ranar 19 ga watan shekarar 2025, in ba haka ba, za ta haramta yin amfani da manhajar a fadin kasar. Sai dai ba a yi zaton hakan ya sa dimbin masu bibiyar shafukan TikTok na kasar ta Amurka za su kama REDnote, a maimakon zabar manhajojin sada zumunta ta cikin gida ba. A game da hakan, wasu daga cikinsu sun ce, dalili shi ne don nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin Amurka ta yi.

  • Ma’aikatar Wajen Sin: Yamadidin Da Ake Yi Na “An Tilasta Wa Mutane Yin Aikin Dole” Karya Ne
  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka

Aria Lynn Grayson, mai bibiyar shafin TikTok ce daga Los Angeles, wadda ta kan samar da hotunan bidiyo game da ilmin kwalliya. A hoton bidiyon da ta bayar a shafinta na REDnote, ta ce, “Gwamnatin kasarmu tana yunkurin haramta yin amfani da TikTok, wai manhajar tana barazana ga tsaron kasa, kuma wai kasar Sin na neman satar bayananmu, amma a hakika kasancewar mu masu ziyartar shafukan yanar gizo, musamman na shafukan TikTok, mun san abubuwan da ke faruwa a duniya.” Sai kuma wata mai bibiyar shafin TikTok da ake kira Amy daga jihar Massachusetts, tana ganin cewa, kasar Sin ba ta sha’awar sanin “me mu ka fi son ci”. Ta ce, “A hakika, gwamnatin kasar Amurka ita ce take sa ido a kan al’ummarta da satar bayananmu.” Ta kara da cewa, aminanta da yawa na TikTok sun sadu da juna a shafin REDnote, “Ina matukar jin dadin yin musaya tare da ‘yan Amurka masu bibiyar TikTok da suka kaura zuwa nan, a ganina tamkar juyin juya hali ne muka yi. Muna jin dadin yin musuyar ra’ayoyi tare da mutanen kasar Sin ta dandalin, duk da kasancewar bambancin al’adu a tsakaninmu.”

ADVERTISEMENT

“Barkanku dai, mutanen kasar Sin, ni dan kasar Amurka ne, idan kuna bukatar taimako wajen koyon Turancin Ingilishi, to, ina nan!” “Barkanmu dai! Ni mai nazarin halittun teku ne daga jihar California, kuma zan so in samu abokai a nan, kuma ina son koyon Sinanci, kuma zan iya taimaka muku koyon Turancin Ingilishi!” “Ko za ku iya nuna min titunan kasar Sin?”…

Kamar yadda Amy ta fada, dimbin masu bibiyar shafin TikTok sun yi musaya sosai tare da masu bibbiyar shafin REDnote, bayan da suka sauke manhajar, inda suke yin amfani da Turanci ko kuma Sinancin da tamkar suka fassara da wata nau’in manhaja, suna nuna harkokin da suka shafi rayuwarsu ta yau da kullum. Kuma masu bibiyar shafin REDnote na kasar Sin ma sun yi musaya sosai tare da su. Akwai kuma wani dan Amurka da ya samu sakwannin fatan alheri kusan dubu biyar daga Sinawa masu bibiyar shafin REDnote, sa’o’i kadan bayan da ya bayyana fatan samun gaisuwar fatan alheri daga mutanen kasar Sin a shafinsa na REDnote a ranar haihuwarsa.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

“A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka a tsakanin Sin da Amurka, an sada sabuwar zumunta a tsakanin kasashen biyu ta wata manhajar da a baya mutanen kasashen waje ba sa amfani da ita sosai.” In ji jaridar Wallstreet Journal. A duk lokacin da take da fifiko a fannin fasahohi, ta kan tabo maganar ‘yancin tattalin arziki, a lokacin da ba ta da shi kuma, sai ta jaddada muhimmancin “tsaron kasa”, wannan mataki ne da gwamnatin kasar Amurka ta saba dauka. Sai dai a wannan karo, al’ummar kasar ba su yarda a kwace hakkinsu ba.

Yau kimanin shekaru 54 da suka gabata, ta diplomasiyyar wasan kwallon tebur, kasashen Sin da Amurka suka bude kofar yin cudanya da juna, tare da farfado da huldarsu, matakin da ya haifar da muhimmin tasiri ga yanayin duniya. Bayan tsawon shekaru 54, a lokacin da huldar kasashen biyu ke kara fuskantar kalubale, muna fatan dandalin REDnote zai zamanto tamkar sabuwar hanyar da za ta kara fahimtar da al’ummar kasar Amurka game da hakikanin yanayin da ake ciki a kasar Sin, da karfafa cudanya a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za a farfado da huldar kasashen biyu, don kwantar da hankulan al’ummar kasashen biyu da na duniya baki daya.

TikTok
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
TikTok
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.