ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa “TikTok Refugee” Na Amurka Suke Ta Kama REDnote Ta Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
TikTok

REDnote wata manhajar sada zumunta ce da ke samun karbuwa a kasar Sin, kuma ni kaina ina bibiyar shafukan REDnote. Sai dai a kwanakin nan, na tarar da dimbin masu bibiyar shafin TikTok da suka fito daga kasar Amurka, wadanda suke kiran kansu “TikTok Refugee”, wadanda ke ta kaura zuwa REDnote, kuma a cewarsu, dalilin hakan shi ne don tinkarar matsalar haramcin da gwamnatin kasar Amurka ka iya sanya wa TikTok.

Lallai a baya, gwamnatin kasar Amurka ta fake da sunan wai “tsaron kasa”, kuma ta bukaci kamfanin Bytedance da ke mallakar TikTok, da ya sayar da TikTok din ga bangaren Amurka kafin ranar 19 ga watan shekarar 2025, in ba haka ba, za ta haramta yin amfani da manhajar a fadin kasar. Sai dai ba a yi zaton hakan ya sa dimbin masu bibiyar shafukan TikTok na kasar ta Amurka za su kama REDnote, a maimakon zabar manhajojin sada zumunta ta cikin gida ba. A game da hakan, wasu daga cikinsu sun ce, dalili shi ne don nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin Amurka ta yi.

  • Ma’aikatar Wajen Sin: Yamadidin Da Ake Yi Na “An Tilasta Wa Mutane Yin Aikin Dole” Karya Ne
  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka

Aria Lynn Grayson, mai bibiyar shafin TikTok ce daga Los Angeles, wadda ta kan samar da hotunan bidiyo game da ilmin kwalliya. A hoton bidiyon da ta bayar a shafinta na REDnote, ta ce, “Gwamnatin kasarmu tana yunkurin haramta yin amfani da TikTok, wai manhajar tana barazana ga tsaron kasa, kuma wai kasar Sin na neman satar bayananmu, amma a hakika kasancewar mu masu ziyartar shafukan yanar gizo, musamman na shafukan TikTok, mun san abubuwan da ke faruwa a duniya.” Sai kuma wata mai bibiyar shafin TikTok da ake kira Amy daga jihar Massachusetts, tana ganin cewa, kasar Sin ba ta sha’awar sanin “me mu ka fi son ci”. Ta ce, “A hakika, gwamnatin kasar Amurka ita ce take sa ido a kan al’ummarta da satar bayananmu.” Ta kara da cewa, aminanta da yawa na TikTok sun sadu da juna a shafin REDnote, “Ina matukar jin dadin yin musaya tare da ‘yan Amurka masu bibiyar TikTok da suka kaura zuwa nan, a ganina tamkar juyin juya hali ne muka yi. Muna jin dadin yin musuyar ra’ayoyi tare da mutanen kasar Sin ta dandalin, duk da kasancewar bambancin al’adu a tsakaninmu.”

ADVERTISEMENT

“Barkanku dai, mutanen kasar Sin, ni dan kasar Amurka ne, idan kuna bukatar taimako wajen koyon Turancin Ingilishi, to, ina nan!” “Barkanmu dai! Ni mai nazarin halittun teku ne daga jihar California, kuma zan so in samu abokai a nan, kuma ina son koyon Sinanci, kuma zan iya taimaka muku koyon Turancin Ingilishi!” “Ko za ku iya nuna min titunan kasar Sin?”…

Kamar yadda Amy ta fada, dimbin masu bibiyar shafin TikTok sun yi musaya sosai tare da masu bibbiyar shafin REDnote, bayan da suka sauke manhajar, inda suke yin amfani da Turanci ko kuma Sinancin da tamkar suka fassara da wata nau’in manhaja, suna nuna harkokin da suka shafi rayuwarsu ta yau da kullum. Kuma masu bibiyar shafin REDnote na kasar Sin ma sun yi musaya sosai tare da su. Akwai kuma wani dan Amurka da ya samu sakwannin fatan alheri kusan dubu biyar daga Sinawa masu bibiyar shafin REDnote, sa’o’i kadan bayan da ya bayyana fatan samun gaisuwar fatan alheri daga mutanen kasar Sin a shafinsa na REDnote a ranar haihuwarsa.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

“A daidai lokacin da ake fuskantar tsamin dangantaka a tsakanin Sin da Amurka, an sada sabuwar zumunta a tsakanin kasashen biyu ta wata manhajar da a baya mutanen kasashen waje ba sa amfani da ita sosai.” In ji jaridar Wallstreet Journal. A duk lokacin da take da fifiko a fannin fasahohi, ta kan tabo maganar ‘yancin tattalin arziki, a lokacin da ba ta da shi kuma, sai ta jaddada muhimmancin “tsaron kasa”, wannan mataki ne da gwamnatin kasar Amurka ta saba dauka. Sai dai a wannan karo, al’ummar kasar ba su yarda a kwace hakkinsu ba.

Yau kimanin shekaru 54 da suka gabata, ta diplomasiyyar wasan kwallon tebur, kasashen Sin da Amurka suka bude kofar yin cudanya da juna, tare da farfado da huldarsu, matakin da ya haifar da muhimmin tasiri ga yanayin duniya. Bayan tsawon shekaru 54, a lokacin da huldar kasashen biyu ke kara fuskantar kalubale, muna fatan dandalin REDnote zai zamanto tamkar sabuwar hanyar da za ta kara fahimtar da al’ummar kasar Amurka game da hakikanin yanayin da ake ciki a kasar Sin, da karfafa cudanya a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za a farfado da huldar kasashen biyu, don kwantar da hankulan al’ummar kasashen biyu da na duniya baki daya.

TikTok
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
TikTok
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.