• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau na karanta wani bayanin da aka wallafa shi a jaridar SCMP ta yankin Hong Kong na Sin, wanda ya yi tsokaci kan yadda karin ‘yan kasuwar kasashen Afirka ke amfani da kudin Sin RMB, maimakon dalar Amurka, wajen ciniki da abokan huldarsu dake kasar Sin.

Cikin bayanin, an yi misali da kasar Kenya, inda a cibiyar kasuwanci ta Eastleigh dake Nairobi, fadar mulkin kasar, ‘yan kasuwa suka kafa wata hanyar biyan kudi don sayen kayayyakin kasar Sin, inda ake biyan kudin kasar Kenya ga wani kamfanin jigilar kaya, daga baya kamfanin zai dauki nauyin biyan kudin Sin RMB ga masu sayar da kayayyaki dake kasar Sin. Ban da haka, an ce a cibiyoyin kasuwanci dake Lagos na Nijeriya ma, ana yin haka wajen gudanar da cinikin waje, wato canza Naira zuwa kudin Sin kai tsaye, sa’an nan a yi amfani da kudin Sin wajen sayen kayayyaki. To, hakan ya nuna wani yanayi na kara yin amfani da kudin Sin RMB wajen gudanar da ciniki a kasashen Afirka.

  • Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
  • Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Sai dai me ya sa ‘yan kasuwan kasashen Afirka ke son amfani da kudin Sin maimakon dalar Amurka, wadda suka fi so a baya? A cikin bayanin jaridar SCMP, an ambachi wasu dalilan da Ovigwe Eguegu, mai nazarin al’amuran siyasa na kasar Najeriya, ya gabatar. Wato da farko, huldar ciniki mai karfi a tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin ta sa ake iya amfani da kudin Sin RMB wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Na biyu kuma shi ne domin halayyar dalar Amurka. A cewar Mista Eguegu, wannan batu ya shafi yadda ake mai da dalar Amurka a matsayin wani nau’in makami, da yunkurin kasar Amurka na lalata huldar ciniki dake tsakanin kasar Sin da sauran kasashe, wanda ke haifar da matsin lamba ga ‘yan kasuwar Afirka, da dai sauransu.

Hakika batun mai da kudin dala makami da Mista Eguegu ya ambata, na nufin yadda kasar Amurka ke amfani da dalar Amurka wajen kwatar dukiyoyin sauran kasashe. Misali, kasar Amurka ta samar da dimbin dala a kasuwa don kyautata yanayin kasuwarta ta hannayen jari, sai dai batun ya sa jama’ar kasashe daban daban fuskantar matsalar hauhawar farashin kayayyaki. Ban da haka, karuwa da raguwar ajiyar kudin ruwa a bankunan kasar Amurka a kai a kai su kan haddasa raguwar darajar kadarorin sauran kasashe, ta yadda kasar Amurka za ta samu damar sayen kadarorin da farashi mai rahusa. Ban da haka, a halin yanzu, kasar Amurka na kara rungumar ra’ayin daukar matakai bisa radin kai, lamarin da zai sanya ta kara amfani da kudin dala a matsayin makami, da haddasa karin matsaloli a sauran kasashe.

Haka zalika, matakan radin kai na kasar Amurka su ma sun girgiza matsayin dalar Amurka sosai. Misali, matakin karbar karin harajin fito kan kayayyakin sauran kasashe da kasar Amurka ta dauka, da nufin kawar da gibin ciniki, yana raunana matsayin dalar Amurka sosai. Saboda, dole ne a kiyaye gibin ciniki da farko, ta yadda sauran kasashe za su samu dalar Amurka a hannunsu, daga baya za a iya dinga amfani da kudin wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Yanzu matakin da kasar Amurka ta dauka shi ne domin neman magance daukar nauyin samar da gibin ciniki, amma hakan tamkar girgiza tushen matsayin kudin dala ne.

Labarai Masu Nasaba

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

Tsohon ministan kudin kasar Amurka John Connally ya ce, dala kudi ne na Amurka, amma matsala ce ga sauran kasashen duniya. Yanzu haka tsarin kudin na haifar da karin radadi ga kasashe daban daban, sakamakon matakan kasar Amurka na kashin kai, lamarin da ya sanya dimbin kasashe neman kauracewa tsarin dalar Amurka. Misali, a rubu’in farkon bana, darajar cinikin da kasar Sin ta yi tare da kasashen Malaysia da Cambodia da kudin RMB, ta karu da kaso 27%, da 24%, bisa makamancin lokacin bara. Kana a nata bangare, kasar Najeriya za ta kulla yarjejeniyar musayar kudin Naira zuwa kudin Sin RMB kai tsaye, tare da kasar Sin, bisa wani labarin da jaridar Vanguard ta kasar Najeriya ta gabatar.

Kudi wani nau’in kayan aiki ne. Idan ana iya amfani da shi cikin sauki, kuma za a iya dogaro a kan sa ba tare da samun hasara ba, to, za a so a yi amfani da shi. Amma idan wani kudi ya kan haifar da matsaloli, to, tabbas za a guji yin amfani da shi. Wannan batu yana cikin tsarin gudanar tattalin arziki, ba wani abu ne da za a iya sauya shi ta karfin siyasa ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Next Post

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Related

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

4 days ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

5 days ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

6 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

1 week ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

2 weeks ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

2 weeks ago
Next Post
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

June 23, 2025
Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

June 23, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

June 23, 2025
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.