ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Yau na karanta wani bayanin da aka wallafa shi a jaridar SCMP ta yankin Hong Kong na Sin, wanda ya yi tsokaci kan yadda karin ‘yan kasuwar kasashen Afirka ke amfani da kudin Sin RMB, maimakon dalar Amurka, wajen ciniki da abokan huldarsu dake kasar Sin.

Cikin bayanin, an yi misali da kasar Kenya, inda a cibiyar kasuwanci ta Eastleigh dake Nairobi, fadar mulkin kasar, ‘yan kasuwa suka kafa wata hanyar biyan kudi don sayen kayayyakin kasar Sin, inda ake biyan kudin kasar Kenya ga wani kamfanin jigilar kaya, daga baya kamfanin zai dauki nauyin biyan kudin Sin RMB ga masu sayar da kayayyaki dake kasar Sin. Ban da haka, an ce a cibiyoyin kasuwanci dake Lagos na Nijeriya ma, ana yin haka wajen gudanar da cinikin waje, wato canza Naira zuwa kudin Sin kai tsaye, sa’an nan a yi amfani da kudin Sin wajen sayen kayayyaki. To, hakan ya nuna wani yanayi na kara yin amfani da kudin Sin RMB wajen gudanar da ciniki a kasashen Afirka.

  • Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
  • Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Sai dai me ya sa ‘yan kasuwan kasashen Afirka ke son amfani da kudin Sin maimakon dalar Amurka, wadda suka fi so a baya? A cikin bayanin jaridar SCMP, an ambachi wasu dalilan da Ovigwe Eguegu, mai nazarin al’amuran siyasa na kasar Najeriya, ya gabatar. Wato da farko, huldar ciniki mai karfi a tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin ta sa ake iya amfani da kudin Sin RMB wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Na biyu kuma shi ne domin halayyar dalar Amurka. A cewar Mista Eguegu, wannan batu ya shafi yadda ake mai da dalar Amurka a matsayin wani nau’in makami, da yunkurin kasar Amurka na lalata huldar ciniki dake tsakanin kasar Sin da sauran kasashe, wanda ke haifar da matsin lamba ga ‘yan kasuwar Afirka, da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Hakika batun mai da kudin dala makami da Mista Eguegu ya ambata, na nufin yadda kasar Amurka ke amfani da dalar Amurka wajen kwatar dukiyoyin sauran kasashe. Misali, kasar Amurka ta samar da dimbin dala a kasuwa don kyautata yanayin kasuwarta ta hannayen jari, sai dai batun ya sa jama’ar kasashe daban daban fuskantar matsalar hauhawar farashin kayayyaki. Ban da haka, karuwa da raguwar ajiyar kudin ruwa a bankunan kasar Amurka a kai a kai su kan haddasa raguwar darajar kadarorin sauran kasashe, ta yadda kasar Amurka za ta samu damar sayen kadarorin da farashi mai rahusa. Ban da haka, a halin yanzu, kasar Amurka na kara rungumar ra’ayin daukar matakai bisa radin kai, lamarin da zai sanya ta kara amfani da kudin dala a matsayin makami, da haddasa karin matsaloli a sauran kasashe.

Haka zalika, matakan radin kai na kasar Amurka su ma sun girgiza matsayin dalar Amurka sosai. Misali, matakin karbar karin harajin fito kan kayayyakin sauran kasashe da kasar Amurka ta dauka, da nufin kawar da gibin ciniki, yana raunana matsayin dalar Amurka sosai. Saboda, dole ne a kiyaye gibin ciniki da farko, ta yadda sauran kasashe za su samu dalar Amurka a hannunsu, daga baya za a iya dinga amfani da kudin wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Yanzu matakin da kasar Amurka ta dauka shi ne domin neman magance daukar nauyin samar da gibin ciniki, amma hakan tamkar girgiza tushen matsayin kudin dala ne.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Tsohon ministan kudin kasar Amurka John Connally ya ce, dala kudi ne na Amurka, amma matsala ce ga sauran kasashen duniya. Yanzu haka tsarin kudin na haifar da karin radadi ga kasashe daban daban, sakamakon matakan kasar Amurka na kashin kai, lamarin da ya sanya dimbin kasashe neman kauracewa tsarin dalar Amurka. Misali, a rubu’in farkon bana, darajar cinikin da kasar Sin ta yi tare da kasashen Malaysia da Cambodia da kudin RMB, ta karu da kaso 27%, da 24%, bisa makamancin lokacin bara. Kana a nata bangare, kasar Najeriya za ta kulla yarjejeniyar musayar kudin Naira zuwa kudin Sin RMB kai tsaye, tare da kasar Sin, bisa wani labarin da jaridar Vanguard ta kasar Najeriya ta gabatar.

Kudi wani nau’in kayan aiki ne. Idan ana iya amfani da shi cikin sauki, kuma za a iya dogaro a kan sa ba tare da samun hasara ba, to, za a so a yi amfani da shi. Amma idan wani kudi ya kan haifar da matsaloli, to, tabbas za a guji yin amfani da shi. Wannan batu yana cikin tsarin gudanar tattalin arziki, ba wani abu ne da za a iya sauya shi ta karfin siyasa ba. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.