ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Yau na karanta wani bayanin da aka wallafa shi a jaridar SCMP ta yankin Hong Kong na Sin, wanda ya yi tsokaci kan yadda karin ‘yan kasuwar kasashen Afirka ke amfani da kudin Sin RMB, maimakon dalar Amurka, wajen ciniki da abokan huldarsu dake kasar Sin.

Cikin bayanin, an yi misali da kasar Kenya, inda a cibiyar kasuwanci ta Eastleigh dake Nairobi, fadar mulkin kasar, ‘yan kasuwa suka kafa wata hanyar biyan kudi don sayen kayayyakin kasar Sin, inda ake biyan kudin kasar Kenya ga wani kamfanin jigilar kaya, daga baya kamfanin zai dauki nauyin biyan kudin Sin RMB ga masu sayar da kayayyaki dake kasar Sin. Ban da haka, an ce a cibiyoyin kasuwanci dake Lagos na Nijeriya ma, ana yin haka wajen gudanar da cinikin waje, wato canza Naira zuwa kudin Sin kai tsaye, sa’an nan a yi amfani da kudin Sin wajen sayen kayayyaki. To, hakan ya nuna wani yanayi na kara yin amfani da kudin Sin RMB wajen gudanar da ciniki a kasashen Afirka.

  • Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
  • Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Sai dai me ya sa ‘yan kasuwan kasashen Afirka ke son amfani da kudin Sin maimakon dalar Amurka, wadda suka fi so a baya? A cikin bayanin jaridar SCMP, an ambachi wasu dalilan da Ovigwe Eguegu, mai nazarin al’amuran siyasa na kasar Najeriya, ya gabatar. Wato da farko, huldar ciniki mai karfi a tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin ta sa ake iya amfani da kudin Sin RMB wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Na biyu kuma shi ne domin halayyar dalar Amurka. A cewar Mista Eguegu, wannan batu ya shafi yadda ake mai da dalar Amurka a matsayin wani nau’in makami, da yunkurin kasar Amurka na lalata huldar ciniki dake tsakanin kasar Sin da sauran kasashe, wanda ke haifar da matsin lamba ga ‘yan kasuwar Afirka, da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Hakika batun mai da kudin dala makami da Mista Eguegu ya ambata, na nufin yadda kasar Amurka ke amfani da dalar Amurka wajen kwatar dukiyoyin sauran kasashe. Misali, kasar Amurka ta samar da dimbin dala a kasuwa don kyautata yanayin kasuwarta ta hannayen jari, sai dai batun ya sa jama’ar kasashe daban daban fuskantar matsalar hauhawar farashin kayayyaki. Ban da haka, karuwa da raguwar ajiyar kudin ruwa a bankunan kasar Amurka a kai a kai su kan haddasa raguwar darajar kadarorin sauran kasashe, ta yadda kasar Amurka za ta samu damar sayen kadarorin da farashi mai rahusa. Ban da haka, a halin yanzu, kasar Amurka na kara rungumar ra’ayin daukar matakai bisa radin kai, lamarin da zai sanya ta kara amfani da kudin dala a matsayin makami, da haddasa karin matsaloli a sauran kasashe.

Haka zalika, matakan radin kai na kasar Amurka su ma sun girgiza matsayin dalar Amurka sosai. Misali, matakin karbar karin harajin fito kan kayayyakin sauran kasashe da kasar Amurka ta dauka, da nufin kawar da gibin ciniki, yana raunana matsayin dalar Amurka sosai. Saboda, dole ne a kiyaye gibin ciniki da farko, ta yadda sauran kasashe za su samu dalar Amurka a hannunsu, daga baya za a iya dinga amfani da kudin wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Yanzu matakin da kasar Amurka ta dauka shi ne domin neman magance daukar nauyin samar da gibin ciniki, amma hakan tamkar girgiza tushen matsayin kudin dala ne.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Tsohon ministan kudin kasar Amurka John Connally ya ce, dala kudi ne na Amurka, amma matsala ce ga sauran kasashen duniya. Yanzu haka tsarin kudin na haifar da karin radadi ga kasashe daban daban, sakamakon matakan kasar Amurka na kashin kai, lamarin da ya sanya dimbin kasashe neman kauracewa tsarin dalar Amurka. Misali, a rubu’in farkon bana, darajar cinikin da kasar Sin ta yi tare da kasashen Malaysia da Cambodia da kudin RMB, ta karu da kaso 27%, da 24%, bisa makamancin lokacin bara. Kana a nata bangare, kasar Najeriya za ta kulla yarjejeniyar musayar kudin Naira zuwa kudin Sin RMB kai tsaye, tare da kasar Sin, bisa wani labarin da jaridar Vanguard ta kasar Najeriya ta gabatar.

Kudi wani nau’in kayan aiki ne. Idan ana iya amfani da shi cikin sauki, kuma za a iya dogaro a kan sa ba tare da samun hasara ba, to, za a so a yi amfani da shi. Amma idan wani kudi ya kan haifar da matsaloli, to, tabbas za a guji yin amfani da shi. Wannan batu yana cikin tsarin gudanar tattalin arziki, ba wani abu ne da za a iya sauya shi ta karfin siyasa ba. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.