• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum, dan Allah Malam Ina bukatar bayani a kan bambancin wadannan Ruwan guda biyu masu fitowa daga gaban mace, watau “KUDRA da kuma SUFRAH”? Allah ya saka da alkhairia.

  • An Bayyana Dalilin Kafa Kungiyar Mawakan Arewa Mai Taken ‘13×13’

Wa’alaykumussalam. To ‘yar’uwa, wannan yana daga cikin mas’aloli masu mutukar muhimanci, amma ga abin da ya sawwka game da haka :
Sufra na nufin mace ta ga ruwa mai fatsi-fatsi kamar ruwan ciwo, ya fito daga gabanta.

Kudra kuwa na nufin: ruwa ya ringa fitowa daga farjin mace, wanda kalarsa take kasancewa tsakanin fatsi-fatsi da baki wato kamar ruwa gurbatacce.
Dangane da hukuncinsu kuwa: idan daya daga cikinsu ya kasance a tsakiyar haila ne ko kuma yana hade da haila kafin ta sami tsarki to wannan ana saka shi a cikin haila, idan kuma bayan tsarki ne to ba haila ba ne saboda fadin Ummu Adiyya “mun kasance ba ma kirga sufra da kudra bayan tsarki a cikin haila”, Abu Dawud ya ruwaito shi da sanadi mai inganci.

A hadisin A’isha kuma (Mata suna aiko mata da abin da suke sawa lokacin da suke haila a jikinsa akwai sufra (wato ruwan da yake kama da ruwan ciwo) sai ta ce musu kada ku yi gaggawa har sai kun ga farin ruwa ya fito, ta yadda za mu yi amfani da hadisin Ummu Adiyya bayan an sami tsarki, ma’ana ko ta ga sufra da kudra ba za ta kirga su a cikin haila ba, hadisin A’isha kuma za mu yi amfani da shi idan tana cikin haila ta yadda za ta kirga da su.

Allah ne mafi sani.

Labarai Masu Nasaba

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

A Karshen Dare Ake Yin Wutiri

Assalamu alaikum wa rahmatullah. Malam mene ne hukuncin yin wuturi a lokacin taraweeh bayan kuma mutum yana son yin tahajjud cikin dare?
Wa’alaikum assalam, in har mutum ya san zai yi wata sallar bayan tarawihi, to abin da yake daidai shi ne ya jinkirta wutirinsa zuwa karshen dare saboda hadisin da Bukari da Muslim suka rawaito cewa: Annabi (SAW) yana barin wutirin sa in ya yi sallar dare zuwa lokacin sahur, da kuma hadisin da Annabin yake cewa: Ku sanya wutiri sallarku ta karshe da daddare”
Bukari ne ya rawaito da Muslim.
Allah ne mafi sani.

Mene Ne Hukuncin Wanda Ya Kashe Kansa Da Gangan?

Assalamu alaikum, Malam mene ne hukunci da matsayin wanda ya kashe kansa ko ya yi sanadiyyar mutuwarsa da kansa, Allah ya kara wa malam ilimi da lafiya. Na gode.
Wa’alaikum assalam, wanda ya kashe kansa da gangan, ranar Alkiyama zai shiga wuta, zai ci gaba da kashe kansa da abin da ya kashe da shi a duniya a cikin wutar lahira mai kuna, kamar yadda ya tabbata a hadisi.
In har ya mutu da imani ko da kwayar zarra ne, ba zai dawwama a cikin wutar ba, zai fita bayan ya gama lokacin da Allah ya diba masa, kamar yadda hadisai suka bayyana.
Allah ne mafi sani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

Next Post

2023: Yarima Ne Kadai Zai Iya Dorawa Da Irin Nasarar Da Buhari Ya Samu A Mulki —Olumide

Related

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Labarai

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

2 hours ago
Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
Labarai

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

2 hours ago
Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 
Labarai

Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 

5 hours ago
FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
Labarai

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

14 hours ago
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

16 hours ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

21 hours ago
Next Post
2023: Yarima Ne Kadai Zai Iya Dorawa Da Irin Nasarar Da Buhari Ya Samu A Mulki —Olumide

2023: Yarima Ne Kadai Zai Iya Dorawa Da Irin Nasarar Da Buhari Ya Samu A Mulki —Olumide

LABARAI MASU NASABA

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

June 22, 2025
Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

June 22, 2025
Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

June 22, 2025
Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

June 22, 2025
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

June 22, 2025
Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 

Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 

June 22, 2025
FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.