• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
in Wasanni
0
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar ƴan wasa mata ta Nijeriya ita ce tawagar ƙwallon ƙafa da masoya ƙwallon ƙafa a ƙasar nan suke farin ciki da ita a ko da yaushe domin a lokuta da dama tana sharewa ƴan Nijeriya hawaya a duk lokacin da suke wakiltar ƙasar nan a gasanni daban-daban na nahiyar Afirka da ma na duniya baki daya wanda hakan kuma babbar nasara ce ga harkokin ƙwallon ƙafa musamman ga matan da suke sha’awar ƙwallon ƙafa a ƙasar nan.

Nijeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo na 10 bayan ta doke mai masaukin baƙi ƙasar Morocco a wasan ƙarshe da aka buga na gasar ta shekara ta 2024, wadda aka jinkirta har ta shigo wannan shekara ta 2025.

Wasan ya tashi ne Nijeriya tana da ci uku ya yin da Morocco ke da biyu bayan an kai ruwa rana a wasan da aka fafata a ƙarshen satin da ya gabata.

  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • Shekaru 15, Wasanni 535, Yaushe Kane Zai Lashe Kofi A Ƙwallon Ƙafa?

Morocco ce ta fara shiga gaba a wasan inda ta zura ƙwallo biyu tun kafin a je hutun rabin lokaci ta ƙafar ƴan wasanta Ghizlane Chebbak da kuma Sanaa Mssoudy. Sai dai bayan komawa daga hutun rabin lokaci Nijeriya ta farke ƙwallon farko ta ƙafar ƴar wasa Esther Okoronkwo kafin dagabisani Folashade Ijamilusi ta zura ƙwallo ta biyu. Kuma wannan ya nuna cewa Nijeriya ta ci gaba da riƙe kambunta a matsayin wadda ta fi nuna bajinta a tarihin gasar.

Karawar ƙarshen ta wakana ne a filin wasa na Olympic Stadium mai cin ƴan kallo dubu 21, 000 da ke birnin Rabat, a shekara ta 2022, Morocco ta zo ta biyu a gasar a wannan filin bayan ta sha kashi a hannun Afirka ta kudu. Tawagar Morocco da ke ƙarƙashin jagorancin mai horaswa Jorge ɓilda, ta so ta dauki kofin a karon farko a tarihi, sai dai hakan bai yiwu ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Nijeriya, wadda take ta daya a jerin ƙasashen da suka fi iya ƙwallon mata a Afirka, ta zura ƙwallon da ta ba ta nasara ne a gab da tashi wasa a karawarta da Afirka ta Kudu a wasan kusa da na ƙarshe. A yanzu za a iya cewa Nijeriya ta cimma burinta na ‘Mission ɗ’, wato lashe kofin a karo na 10 a tarihi kuma ta ci gaba da jan zarenta na tawagar mata wadda babu kamarta a wannan nahiyar.

Nijeriya ta ƙara kafa wani tarihin kasancewar ita ce ta farko da ta lashe sabon kofin na gasar bayan sauya shi da aka yi daga wanda aka saba amfani da shi a baya. A ƙarshen wasan Rasheedat Ajibade ta Nijeriya ce ta lashe kyautar ƴar wasa mafi ƙwazo a gasar ta 2024 sai yar wasan Morocco Ghizlane Chebbak, wadda  ta zama wadda ta fi kowa zura ƙwallo a gasar, inda ta zura ƙwallaye biyar.

Mai tsaron raga ta Nijeriya Chiamaka Nnadozie ce ta karɓi kyautar mai tsaron raga mafi ƙwazo, inda aka zura ƙwallo a ragarta sau uku kacal tun bayan fara gasar ta wannan shekara. Ita kuwa Esther Okoronkwo ta zama gwarzuwar karawar, wannan ba abin mamaki ba ne ganin irin gudumawar da ta bayar wajen samun nasara Nijeriya. Ta zura ƙwallo daya sannan ta taimaka aka ci sauran biyun.

Baya ga kofin, Nijeriya za ta koma gida da ladan kuɗi dala miliyan daya kamar yadda hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka CAF, ta yi alƙawarin bawa duk tawagar da ta samu nasara.

Jerin ƴan Wasan Nijeriya Mata da Babu Kamarsu

Abu na farko da mutum zai fara ji game da tawagar ƙwallon ƙafa ta matan Nijeriya shi ne ta lashe kofin ƙasashen Afirka sau 10, mafi yawa kenan a tarihin gasar ga kowace ƙasa. Hakan ta sa dole ake cewa tawagar ta Super Falcons ce mafi hazaƙa a nahiyar Afirka saboda sauran nasarori da ta samu tun daga kafa ta a shekarun 1990. Gabanin gasar kofin Afirka ta 2024 a Morocco, Super Falcons ta samu gurbi ne da gagarumar nasara gida da waje a kan Cape ɓerde da ci 5-0 da kuma 2-1.

ƴanmatan na Nijeriya sun lashe kofin Afirka na Wafcon karon farko a 1998, kuma karo na ƙarshe da suka yi hakan shi ne a 2018 – kafin su lashe na ranar Asabar. Hakan na nufin sun lashe gasar sau 10 cikin 13 da suka halarta kuma babu wata ƙasa a tarihin nahiyar Afirka da ta taɓa lashe kofin nahiyar Afirka sau goma a tarihin fara kofin.

Mun yi duba a ƙasan wasu ƴan wasan Nijeriya mata da suka taka rawar gani a baya:

Perpetua Nkwocha

ƴar wasa Perpetua Ijeoma Nkwocha ƴarwasan tsakiya ce da ta yi ritaya daga tawagar ta Super Falcons a 2012. Ita ce kan gaba a ci wa tawagar Nijeriya ƙwallaye inda ta zura ƙwallaye 80 da ta zira a raga cikin wasanni 99 da ta buga. An haife ta a shekarar 1976 kuma ta ci wa Nijeriya ƙwallo huɗu a wasan ƙarshe na gasar kofin Afirka ta mata ta

2004, inda suka doke Kamaru.

Ta lashe kyautar gwarzuwar ƴarƙwallon Afirka har sau huɗu: a 2004, da 2005, da 2010, da kuma 2011. daga cikin ƙungiyoyin da ta bugawa wasa akwai Sunnanå SK ta Sweden, da kuma Clemensnäs IF inda a yanzu take horar da ƴanwasan ƙungiyar bayan ta yi ritaya.

Asisat Oshoala

ƴarƙwallon da ake yi wa kallon daya daga cikin mafiya hazaƙa a tarihin Afirka, Oshoala ta lashe kyautar gwarzuwar Afirka sau shida. ƴarwasan gaban mai shekara 30 ta fara buga wa Nijeriya wasa a watan Satumban 2013. Ta ci kofin Afirka na mata a 2014, da 2016, da 2018. A 2014, ta zama gwarzuwar gasar kofin duniya ta ƴan ƙasa da shekara 20 kuma wadda ta fi zira ƙwallaye a gasar.

Ta buga wasa a ƙungiyoyi da dama, wadanda suka hada da Liɓerpool da Arsenal da Barcelona, da dalian ƙuanjian. Yanzu tana buga wa ƙungiyar Bay FC ta Amurka. daga cikin kyautukan da ta ci akwai gwarzuwar ƴarƙwallon Afirka a shekarun 2014, 2016, 2017, 2019, 2022, 2023.

Rasheedat Ajibade

ƴar ƙwallon da ke bugawa ƙungiyar Atletico Madrid ta Sifaniya wasa, Rasheedat Ajibade ce kyaftin ɗin tawagar Nijeriya yanzu haka. ƴar wasan mai shekara 25 tana da ƙwarewar buga lambobi da dama, ciki har da gefen hagu ko dama ko kuma tsakiya. Ta wakilci Nijeriya a tawagar matasa ta ƴan ƙasa da shekara 17, da 20, kuma ta ci kofin ƙasashen Afirka na mata a 2018. An zaɓe ta matashiyar ƴarwasa mafi hazaƙa a Nijeriya a 2018.

Mercy Akide

Mercy Joy Akide Udoh tsohuwar ƴarwasa ce da ta fara bugawa Nijeriya wasa ne a shekarar 1994, yanzu tana da shekara 49, ƴarwasan tsakiya ce da ta samu nasarar lashe kofin ƙasashen Afirka karo uku a 1998, da 2000, da kuma 2002. Haka nan, ta lashe kyautar gwarzuwar ƴarƙwallon Afirka a 2004.

Francisca Ordega

Francisca Ordega mai shekara 31 na buga wasa a ƙungiyar Al-Ittihad ta Saudiyya a matsayin ƴarwasan gaba. Ta bugawa Nijeriya wasa a dukkan tawagogi tun daga ƴan ƙasa da shekara 17, inda ta buga kofin duniya a tawagar manya a 2011, da 2015, da 2019 sannan tana cikin tawagar Super Falcons da ta lashe kofin Afirka na 2010 da 2014.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FIFAFOOTBALLNijeriyaSuper Falcons
ShareTweetSendShare
Previous Post

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Next Post

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Related

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida
Wasanni

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

1 day ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

2 days ago
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
Wasanni

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

5 days ago
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
Wasanni

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

6 days ago
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
Wasanni

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

7 days ago
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
Wasanni

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

1 week ago
Next Post
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.