ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
Morocco

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Morocco (FRMF) ta shigar da takardar ƙorafi a hukumance zuwa hukumar ƙwallon ƙafa ta Afrika (CAF), tana zargin “rashin adalci daga alƙalin wasa” a wasan ƙarshe na gasar cin kofin mata ta Afrika (WAFCON) da aka fafata tsakaninta da Super Falcons ta Nijeriya.

Kamar yadda jaridar Morocco World News ta ruwaito, FRMF ta bayyana cewa alƙaliyar wasan ta fasa bayar da hukuncin bugun daga kai sai mai tsaron gida (penalty) a minti na 82 da wasan ke 2-2, wanda suka ce ya kamata a baiwa tawagar su.

  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Bidiyon da aka sake dubawa ya nuna yiwuwar cewa ƴar wasan baya ta Nijeriya, Tosin Demehin, ta taɓa ƙwallo da hannu, amma bayan nazarin na’urar VAR, alƙaliyar ta soke hukuncin farko da ta yanke. Wannan mataki ya fusata ‘yan wasan Morocco da masu horas da su, inda suka ce hakan ya shafi sakamakon wasan da Nijeriya ta samu nasara da ci 3-2.

ADVERTISEMENT

Kocin Morocco, Jorge Vilda, wanda ya jagoranci ƙasar Spain zuwa nasara a gasar cin kofin duniya ta mata a 2023, ya bayyana cewa: “Ƙaramin kuskure ne ya sa muka rasa wasan.” Duk da cewa bai saba magana kan alƙalanci ba, Vilda ya amince cewa gajiya ta taka rawa a durƙusar da tawagarsa a zagaye na biyu.

A nasa ɓangaren, kocin Nijeriya, Justine Madugu, ya yabawa Morocco bisa ƙoƙarin da suka nuna a rabin lokacin farko, yana mai cewa sauye-sauyen da suka yi a rabin lokaci na biyu ne suka sauya akalar wasan.

LABARAI MASU NASABA

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

A cewarsa: “Canje-canjen sun taka muhimmiyar rawa.” An buga wasan ƙarshe a filin wasa na Rabat Olympic Stadium, inda Morocco ta fara da ci 2-0, amma Nijeriya ta dawo da ƙwallaye daga Esther Okoronkwo, Folashade Ijamilusi, da ƴar canji Jennifer Echegini. Wannan nasara ta baiwa Super Falcons nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10 – mafi yawa a tarihin gasar.

Morocco
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus
  • Abubakar Sulaiman
    Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

MASU ALAKA

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
Wasanni

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

July 10, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.