ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

by Abba Ibrahim Wada
12 months ago
Mata

Tawagar ƴan wasa mata ta Nijeriya ita ce tawagar ƙwallon ƙafa da masoya ƙwallon ƙafa a ƙasar nan suke farin ciki da ita a ko da yaushe domin a lokuta da dama tana sharewa ƴan Nijeriya hawaya a duk lokacin da suke wakiltar ƙasar nan a gasanni daban-daban na nahiyar Afirka da ma na duniya baki daya wanda hakan kuma babbar nasara ce ga harkokin ƙwallon ƙafa musamman ga matan da suke sha’awar ƙwallon ƙafa a ƙasar nan.

Nijeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo na 10 bayan ta doke mai masaukin baƙi ƙasar Morocco a wasan ƙarshe da aka buga na gasar ta shekara ta 2024, wadda aka jinkirta har ta shigo wannan shekara ta 2025.

Wasan ya tashi ne Nijeriya tana da ci uku ya yin da Morocco ke da biyu bayan an kai ruwa rana a wasan da aka fafata a ƙarshen satin da ya gabata.

ADVERTISEMENT
  • Girgizar Ƙasa: Mutum 1,700 Sun Rasu, 3,400 Sun Jikkata A Myanmar
  • Shekaru 15, Wasanni 535, Yaushe Kane Zai Lashe Kofi A Ƙwallon Ƙafa?

Morocco ce ta fara shiga gaba a wasan inda ta zura ƙwallo biyu tun kafin a je hutun rabin lokaci ta ƙafar ƴan wasanta Ghizlane Chebbak da kuma Sanaa Mssoudy. Sai dai bayan komawa daga hutun rabin lokaci Nijeriya ta farke ƙwallon farko ta ƙafar ƴar wasa Esther Okoronkwo kafin dagabisani Folashade Ijamilusi ta zura ƙwallo ta biyu. Kuma wannan ya nuna cewa Nijeriya ta ci gaba da riƙe kambunta a matsayin wadda ta fi nuna bajinta a tarihin gasar.

Karawar ƙarshen ta wakana ne a filin wasa na Olympic Stadium mai cin ƴan kallo dubu 21, 000 da ke birnin Rabat, a shekara ta 2022, Morocco ta zo ta biyu a gasar a wannan filin bayan ta sha kashi a hannun Afirka ta kudu. Tawagar Morocco da ke ƙarƙashin jagorancin mai horaswa Jorge ɓilda, ta so ta dauki kofin a karon farko a tarihi, sai dai hakan bai yiwu ba.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Nijeriya, wadda take ta daya a jerin ƙasashen da suka fi iya ƙwallon mata a Afirka, ta zura ƙwallon da ta ba ta nasara ne a gab da tashi wasa a karawarta da Afirka ta Kudu a wasan kusa da na ƙarshe. A yanzu za a iya cewa Nijeriya ta cimma burinta na ‘Mission ɗ’, wato lashe kofin a karo na 10 a tarihi kuma ta ci gaba da jan zarenta na tawagar mata wadda babu kamarta a wannan nahiyar.

Nijeriya ta ƙara kafa wani tarihin kasancewar ita ce ta farko da ta lashe sabon kofin na gasar bayan sauya shi da aka yi daga wanda aka saba amfani da shi a baya. A ƙarshen wasan Rasheedat Ajibade ta Nijeriya ce ta lashe kyautar ƴar wasa mafi ƙwazo a gasar ta 2024 sai yar wasan Morocco Ghizlane Chebbak, wadda  ta zama wadda ta fi kowa zura ƙwallo a gasar, inda ta zura ƙwallaye biyar.

Mai tsaron raga ta Nijeriya Chiamaka Nnadozie ce ta karɓi kyautar mai tsaron raga mafi ƙwazo, inda aka zura ƙwallo a ragarta sau uku kacal tun bayan fara gasar ta wannan shekara. Ita kuwa Esther Okoronkwo ta zama gwarzuwar karawar, wannan ba abin mamaki ba ne ganin irin gudumawar da ta bayar wajen samun nasara Nijeriya. Ta zura ƙwallo daya sannan ta taimaka aka ci sauran biyun.

Baya ga kofin, Nijeriya za ta koma gida da ladan kuɗi dala miliyan daya kamar yadda hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka CAF, ta yi alƙawarin bawa duk tawagar da ta samu nasara.

Jerin ƴan Wasan Nijeriya Mata da Babu Kamarsu

Abu na farko da mutum zai fara ji game da tawagar ƙwallon ƙafa ta matan Nijeriya shi ne ta lashe kofin ƙasashen Afirka sau 10, mafi yawa kenan a tarihin gasar ga kowace ƙasa. Hakan ta sa dole ake cewa tawagar ta Super Falcons ce mafi hazaƙa a nahiyar Afirka saboda sauran nasarori da ta samu tun daga kafa ta a shekarun 1990. Gabanin gasar kofin Afirka ta 2024 a Morocco, Super Falcons ta samu gurbi ne da gagarumar nasara gida da waje a kan Cape ɓerde da ci 5-0 da kuma 2-1.

ƴanmatan na Nijeriya sun lashe kofin Afirka na Wafcon karon farko a 1998, kuma karo na ƙarshe da suka yi hakan shi ne a 2018 – kafin su lashe na ranar Asabar. Hakan na nufin sun lashe gasar sau 10 cikin 13 da suka halarta kuma babu wata ƙasa a tarihin nahiyar Afirka da ta taɓa lashe kofin nahiyar Afirka sau goma a tarihin fara kofin.

Mun yi duba a ƙasan wasu ƴan wasan Nijeriya mata da suka taka rawar gani a baya:

Perpetua Nkwocha

ƴar wasa Perpetua Ijeoma Nkwocha ƴarwasan tsakiya ce da ta yi ritaya daga tawagar ta Super Falcons a 2012. Ita ce kan gaba a ci wa tawagar Nijeriya ƙwallaye inda ta zura ƙwallaye 80 da ta zira a raga cikin wasanni 99 da ta buga. An haife ta a shekarar 1976 kuma ta ci wa Nijeriya ƙwallo huɗu a wasan ƙarshe na gasar kofin Afirka ta mata ta

2004, inda suka doke Kamaru.

Ta lashe kyautar gwarzuwar ƴarƙwallon Afirka har sau huɗu: a 2004, da 2005, da 2010, da kuma 2011. daga cikin ƙungiyoyin da ta bugawa wasa akwai Sunnanå SK ta Sweden, da kuma Clemensnäs IF inda a yanzu take horar da ƴanwasan ƙungiyar bayan ta yi ritaya.

Asisat Oshoala

ƴarƙwallon da ake yi wa kallon daya daga cikin mafiya hazaƙa a tarihin Afirka, Oshoala ta lashe kyautar gwarzuwar Afirka sau shida. ƴarwasan gaban mai shekara 30 ta fara buga wa Nijeriya wasa a watan Satumban 2013. Ta ci kofin Afirka na mata a 2014, da 2016, da 2018. A 2014, ta zama gwarzuwar gasar kofin duniya ta ƴan ƙasa da shekara 20 kuma wadda ta fi zira ƙwallaye a gasar.

Ta buga wasa a ƙungiyoyi da dama, wadanda suka hada da Liɓerpool da Arsenal da Barcelona, da dalian ƙuanjian. Yanzu tana buga wa ƙungiyar Bay FC ta Amurka. daga cikin kyautukan da ta ci akwai gwarzuwar ƴarƙwallon Afirka a shekarun 2014, 2016, 2017, 2019, 2022, 2023.

Rasheedat Ajibade

ƴar ƙwallon da ke bugawa ƙungiyar Atletico Madrid ta Sifaniya wasa, Rasheedat Ajibade ce kyaftin ɗin tawagar Nijeriya yanzu haka. ƴar wasan mai shekara 25 tana da ƙwarewar buga lambobi da dama, ciki har da gefen hagu ko dama ko kuma tsakiya. Ta wakilci Nijeriya a tawagar matasa ta ƴan ƙasa da shekara 17, da 20, kuma ta ci kofin ƙasashen Afirka na mata a 2018. An zaɓe ta matashiyar ƴarwasa mafi hazaƙa a Nijeriya a 2018.

Mercy Akide

Mercy Joy Akide Udoh tsohuwar ƴarwasa ce da ta fara bugawa Nijeriya wasa ne a shekarar 1994, yanzu tana da shekara 49, ƴarwasan tsakiya ce da ta samu nasarar lashe kofin ƙasashen Afirka karo uku a 1998, da 2000, da kuma 2002. Haka nan, ta lashe kyautar gwarzuwar ƴarƙwallon Afirka a 2004.

Francisca Ordega

Francisca Ordega mai shekara 31 na buga wasa a ƙungiyar Al-Ittihad ta Saudiyya a matsayin ƴarwasan gaba. Ta bugawa Nijeriya wasa a dukkan tawagogi tun daga ƴan ƙasa da shekara 17, inda ta buga kofin duniya a tawagar manya a 2011, da 2015, da 2019 sannan tana cikin tawagar Super Falcons da ta lashe kofin Afirka na 2010 da 2014.

Mata
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.