• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ƙaddamar Da Shugabannin NIPR, Ya Jaddada Buƙatar Aiki Tare

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Minista Ya Ƙaddamar Da Shugabannin NIPR, Ya Jaddada Buƙatar Aiki Tare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada tabbacin yin aiki tare da Cibiyar Ƙwararru Kan Hulɗa Da Jama’a Da Yaɗa Labarai (NIPR) wajen tsare-tsaren hanyoyin sadarwar da za su tabbatar da cimma nasarar Ajandar Sabon Ƙudiri ta gwamnatin Tinubu.

Idris ya yi wannan tabbaci ne lokacin da ya ke jawabi a wurin rantsar da mambobin Hukumar Gudanarwar NIPR a ranar Talata a Abuja.

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Yaba Da Abota Da Goyon Bayan Juna Da Togo
  • AFCON 2023: Tauraron Super Eagles Na Fama Da Guba Gabanin Wasa Da Cote d’Ivoire

Wannan bayani ya na ƙunshe a cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Minista, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Talata.

Idris ya ce: “A matsayi na na ɗan wannan cibiyar, na fahimci muhimmancin kare martaba da ƙima. To kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai ta ƙudirta yin aiki tare da wannan cibiya domin shata tsare-tsaren sadarwa da yaɗa labarai, waɗanda za su zaburar da Ajandar Sabon Ƙudiri ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Tilas in bayyana maku cewa na yi matuƙar gamsuwa da irin tsare-tsaren da majalisar NIPR ta fito da su, a ƙarƙashin Dakta Ike Neliaku, kamar yadda aka nuna min kafin fara wannan taron.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

“Ina da yaƙinin cewa matuƙar aka aiwatar da waɗannan tsare-tsare, to duk su na da karsashin da za su ɗabbaƙa wannan cibiya, kuma su ɗaukaka wannan ƙasa a idon duniya.”

Ministan ya ɗora wa cibiyar nauyin sake farfaɗo da ƙima da martabar Nijeriya a duniya, ya ce darajar kowace ƙasa ita ce tushe ko ginshiƙin gina ƙasar.

Ya ƙara da cewa daga cikin ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta, akwai abin da ya kira rashin ɗaukar ‘yan ƙasar da ita kan ta ƙasa da wata ƙima. Wannan kuma a cewar sa ba komai ya janyo hakan ba sai mummunar fassara da bahaguwar fahimtar da ake mana a faɗin duniya.

Ya ce: “Wannan kuma abu ne mai ɓacin rai a matsayin mu na ƙwararru. Don haka tilas mu bijiro da hanyoyin da za su kasance mafita, waɗanda za mu nuna wa duniya irin baiwa, daraja, ƙima da martabar da wannan ƙasaitacciyar ƙasa Nijeriya ke da ita.

“Sauran ƙasashe ma kowace na da nata matsalolin, amma inda bambancin yake shi ne ta yadda su ke tunkarar daƙile wani aibi.
“Wannan kuwa abu ne da ake iya cimma nasarar sa ta hanyar haɗa kai tsakanin gwamnati da ƙwararru irin NIPR da kuma kishin ‘yan ƙasa.”

Daga nan ya jinjina wa nagartattun mutanen da su ka kafa cibiyar shekaru 60 da su ka gabata, ta yadda yanzu har ta na ɗaya daga cikin cibiyoyin ƙwararru ƙalilan da ake da su a duniya, waɗanda gwamnati ta yi amanna da su ɗari bisa ɗari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar NIPRMinistan yada labaraiSabon kudiri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya

Next Post

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Related

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

54 minutes ago
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

3 hours ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

4 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

12 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

13 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

15 hours ago
Next Post
Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma'adanai

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.