ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ƙaddamar Da Shugabannin NIPR, Ya Jaddada Buƙatar Aiki Tare

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada tabbacin yin aiki tare da Cibiyar Ƙwararru Kan Hulɗa Da Jama’a Da Yaɗa Labarai (NIPR) wajen tsare-tsaren hanyoyin sadarwar da za su tabbatar da cimma nasarar Ajandar Sabon Ƙudiri ta gwamnatin Tinubu.

Idris ya yi wannan tabbaci ne lokacin da ya ke jawabi a wurin rantsar da mambobin Hukumar Gudanarwar NIPR a ranar Talata a Abuja.

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Yaba Da Abota Da Goyon Bayan Juna Da Togo
  • AFCON 2023: Tauraron Super Eagles Na Fama Da Guba Gabanin Wasa Da Cote d’Ivoire

Wannan bayani ya na ƙunshe a cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Minista, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Idris ya ce: “A matsayi na na ɗan wannan cibiyar, na fahimci muhimmancin kare martaba da ƙima. To kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai ta ƙudirta yin aiki tare da wannan cibiya domin shata tsare-tsaren sadarwa da yaɗa labarai, waɗanda za su zaburar da Ajandar Sabon Ƙudiri ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Tilas in bayyana maku cewa na yi matuƙar gamsuwa da irin tsare-tsaren da majalisar NIPR ta fito da su, a ƙarƙashin Dakta Ike Neliaku, kamar yadda aka nuna min kafin fara wannan taron.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

“Ina da yaƙinin cewa matuƙar aka aiwatar da waɗannan tsare-tsare, to duk su na da karsashin da za su ɗabbaƙa wannan cibiya, kuma su ɗaukaka wannan ƙasa a idon duniya.”

Ministan ya ɗora wa cibiyar nauyin sake farfaɗo da ƙima da martabar Nijeriya a duniya, ya ce darajar kowace ƙasa ita ce tushe ko ginshiƙin gina ƙasar.

Ya ƙara da cewa daga cikin ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta, akwai abin da ya kira rashin ɗaukar ‘yan ƙasar da ita kan ta ƙasa da wata ƙima. Wannan kuma a cewar sa ba komai ya janyo hakan ba sai mummunar fassara da bahaguwar fahimtar da ake mana a faɗin duniya.

Ya ce: “Wannan kuma abu ne mai ɓacin rai a matsayin mu na ƙwararru. Don haka tilas mu bijiro da hanyoyin da za su kasance mafita, waɗanda za mu nuna wa duniya irin baiwa, daraja, ƙima da martabar da wannan ƙasaitacciyar ƙasa Nijeriya ke da ita.

“Sauran ƙasashe ma kowace na da nata matsalolin, amma inda bambancin yake shi ne ta yadda su ke tunkarar daƙile wani aibi.
“Wannan kuwa abu ne da ake iya cimma nasarar sa ta hanyar haɗa kai tsakanin gwamnati da ƙwararru irin NIPR da kuma kishin ‘yan ƙasa.”

Daga nan ya jinjina wa nagartattun mutanen da su ka kafa cibiyar shekaru 60 da su ka gabata, ta yadda yanzu har ta na ɗaya daga cikin cibiyoyin ƙwararru ƙalilan da ake da su a duniya, waɗanda gwamnati ta yi amanna da su ɗari bisa ɗari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma'adanai

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.