• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ƙaddamar Da Shugabannin NIPR, Ya Jaddada Buƙatar Aiki Tare

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Minista Ya Ƙaddamar Da Shugabannin NIPR, Ya Jaddada Buƙatar Aiki Tare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada tabbacin yin aiki tare da Cibiyar Ƙwararru Kan Hulɗa Da Jama’a Da Yaɗa Labarai (NIPR) wajen tsare-tsaren hanyoyin sadarwar da za su tabbatar da cimma nasarar Ajandar Sabon Ƙudiri ta gwamnatin Tinubu.

Idris ya yi wannan tabbaci ne lokacin da ya ke jawabi a wurin rantsar da mambobin Hukumar Gudanarwar NIPR a ranar Talata a Abuja.

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Yaba Da Abota Da Goyon Bayan Juna Da Togo
  • AFCON 2023: Tauraron Super Eagles Na Fama Da Guba Gabanin Wasa Da Cote d’Ivoire

Wannan bayani ya na ƙunshe a cikin sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Minista, Rabi’u Ibrahim ya fitar a ranar Talata.

Idris ya ce: “A matsayi na na ɗan wannan cibiyar, na fahimci muhimmancin kare martaba da ƙima. To kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai ta ƙudirta yin aiki tare da wannan cibiya domin shata tsare-tsaren sadarwa da yaɗa labarai, waɗanda za su zaburar da Ajandar Sabon Ƙudiri ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Tilas in bayyana maku cewa na yi matuƙar gamsuwa da irin tsare-tsaren da majalisar NIPR ta fito da su, a ƙarƙashin Dakta Ike Neliaku, kamar yadda aka nuna min kafin fara wannan taron.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

“Ina da yaƙinin cewa matuƙar aka aiwatar da waɗannan tsare-tsare, to duk su na da karsashin da za su ɗabbaƙa wannan cibiya, kuma su ɗaukaka wannan ƙasa a idon duniya.”

Ministan ya ɗora wa cibiyar nauyin sake farfaɗo da ƙima da martabar Nijeriya a duniya, ya ce darajar kowace ƙasa ita ce tushe ko ginshiƙin gina ƙasar.

Ya ƙara da cewa daga cikin ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta, akwai abin da ya kira rashin ɗaukar ‘yan ƙasar da ita kan ta ƙasa da wata ƙima. Wannan kuma a cewar sa ba komai ya janyo hakan ba sai mummunar fassara da bahaguwar fahimtar da ake mana a faɗin duniya.

Ya ce: “Wannan kuma abu ne mai ɓacin rai a matsayin mu na ƙwararru. Don haka tilas mu bijiro da hanyoyin da za su kasance mafita, waɗanda za mu nuna wa duniya irin baiwa, daraja, ƙima da martabar da wannan ƙasaitacciyar ƙasa Nijeriya ke da ita.

“Sauran ƙasashe ma kowace na da nata matsalolin, amma inda bambancin yake shi ne ta yadda su ke tunkarar daƙile wani aibi.
“Wannan kuwa abu ne da ake iya cimma nasarar sa ta hanyar haɗa kai tsakanin gwamnati da ƙwararru irin NIPR da kuma kishin ‘yan ƙasa.”

Daga nan ya jinjina wa nagartattun mutanen da su ka kafa cibiyar shekaru 60 da su ka gabata, ta yadda yanzu har ta na ɗaya daga cikin cibiyoyin ƙwararru ƙalilan da ake da su a duniya, waɗanda gwamnati ta yi amanna da su ɗari bisa ɗari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar NIPRMinistan yada labaraiSabon kudiri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Bai Wa Emefiele Damar Yin Tafiye-tafiye A Nijeriya

Next Post

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

21 minutes ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

2 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

2 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

4 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

6 hours ago
Next Post
Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma'adanai

LABARAI MASU NASABA

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

June 5, 2025
Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.