• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

by Sulaiman
4 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da kamfen na wayar da kan ɗaliban makarantun sakandare kan kafofin sadarwa da yadda ake amfani da su ta hanyar da ta dace.

Da yake jawabi a taron TEDxNTICAbujaYouth 2025 da aka gudanar a makarantar Nigerian Tulip International College, Abuja, a ranar Asabar, ministan ya jaddada yadda kafafen sada zumunta suke da tasiri ga matasa, tare da buƙatar koya masu dabarun tantance sahihancin bayanan da suke karantawa da watsawa a intanet.

  • Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
  • Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Ya ce: “Saboda ina cikin harkar sadarwa, na kasance mai matuƙar sha’awar yadda mutane suke yaɗa labarai, da yadda mutane za su iya sadar da juna cikin ɗan lokaci kaɗan daga ko’ina cikin duniya, sannan kafin mu ankara sai ga sararin sadarwar dijital ya buɗe. Yanzu akwai Instagram, Facebook, WhatsApp, X da sauran su, amma kuma wannan ma wani ƙalubale ne. Yanzu sadarwa maimakon ta zama abin haɗin kai, tana iya zama abin da za a yi amfani da ta ta hanya mara kyau.”

Ya ƙara da cewa, “Haɓakar duniyar dijital ita ma ta kawo zamanin yaɗa labaran ƙarya, da ruɗani da yaɗa bayanan da ba su da tushe.”

Da yake magana kan jigon taron mai taken “Shauƙi”, Idris ya ba da tarihin rayuwar sa, inda ya bayyana irin shauƙin da ya ke da shi tun yana matashi wajen zama ɗan jaridar gidan rediyo ko talbijin, sai dai wata matsala a gidan su ta tilasta masa shiga jami’a kafin ya cimma burin sa.

Labarai Masu Nasaba

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Ya ce: “A yau ni ne Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya. Ba kawai ɗan watsa shirye-shirye ba ne ni, ni ne babban mai magana da yawun gwamnatin Nijeriya.

“Don haka za ka ga yadda burin da ake ganin kamar an kashe shi shekaru da dama da suka wuce, ya dawo ya amfanar.”

Ya ce kafin ya zama minista, ya mallaki tashar rediyo da talbijin har ma da gidan jarida.

Ministan ya buƙaci matasa da kada su yi watsi da burin su ko da ba sa ganin damar cimma buƙatar su. Ya ce shauƙin sa ne yake motsa shi wajen yaƙi da yaɗuwar labaran ƙarya ta hanyar ƙarfafa fahimtar kafofin sadarwa.

Idris ya kuma bayyana cewa daga watan Nuwamba mai zuwa, Nijeriya za ta fara gudanar da Cibiyar Ilimin Kafofin Sadarwa ta UNESCO mai Mataki na 2.

Ya ce: “Ni ne na jagoranci Nijeriya wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Sadarwa ta UNESCO Category 2 – wadda ita ce irin ta ta farko a duniya – kuma za a kafa ta a Abuja. Zuwa watan Nuwamba idan hukumar UNESCO ta bayar da amincewar ƙarshe, duk duniya za ta dinga kallon Nijeriya.”

Ya ƙara da cewa, “Don haka ba wai kawai ku matasa maza da mata ku ɗauki makirfo, kwamfuta ko wayoyin ku na zamani ku fara faɗin duk abin da kuka ga dama ba ne. Kuna iya samun ilimi, amma kuma kuna buƙatar fahimtar yadda kafofin sadarwa suke.”

An tsara cibiyar ne don koyar da matasa daga Nijeriya da ƙasashen waje dabarun amfani da kafofin sadarwa cikin basira tare da yin kaffa-kaffa da kuma kare kan su daga labaran ƙarya da yaɗuwar bayanan da ba su da tushe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Next Post

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

Related

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Labarai

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

4 minutes ago
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

2 hours ago
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 
Labarai

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

3 hours ago
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

4 hours ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

17 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

19 hours ago
Next Post
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

LABARAI MASU NASABA

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.