ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Tarihi

Bikin murnar cika shekaru 80 da cimma nasarar babban yakin kare kasa na tsohuwar tarayyar Soviet da aka gudanar kwanan nan a birnin Moscow na kasar Rasha, ya sake tunatar da al’ummomin duniya game da abubuwan da suka wakana a tarihi. Yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar da ziyarar aiki a kasar Rasha a daidai wannan lokaci tare da halartar bikin yana da ma’ana mai matukar muhimmanci, wanda ya isar da sakon kasar Sin ga duniya, wato har kullum kasar tana tsayawa tsayin daka a kan kiyaye tsarin duniya, kuma kullum tana daukar nauyin da ke bisa wuyanta na gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya.  

Tarihi tamkar madubi ne. A yakin da aka gudanar a tsakanin masu kishin adalci da masu zalunci yau da kimanin shekaru 80 da suka wuce, da Sin da Rasha sun kasance muhimman fagage na yakin a Asiya da kuma Turai, wadanda suka ba da gudummawa mai matukar muhimmanci wajen cimma nasarar yakar ‘yan “Fascist” a duniya. Sai dai har bayan wucewar shekaru 80, ba a kai ga kawo karshen nuna fin karfi a duniya ba, inda ra’ayin kashin kai, da yin fito na fito a tsakanin kasa da kasa ke ci gaba da addabar duniya.

  • Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

A kwanakin baya, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da tsai da ranar 8 ga watan Mayun kowace shekara a matsayin “ranar nasarar Amurka”, kuma a cewarsa, “Ko kana so ko ba ka so, sabo da mu ne aka kai ga samun nasarar”, “tankoki da jiragen yaki, da manyan motoci, da jiragen sama, da kuma sojoji na kasar Amurka ne suka ci nasara a kan makiya a shekaru 80 da suka wuce. Idan babu Amurka, to sam sam ba nasarar yakin.” Lallai furucin na shugaba Trump da ya mai da nasarar da kasa da kasa suka samu a matsayin gudummawar da Amurka ita kadai ta bayar, ya sake shaida mana nuna fin karfi da kasar Amurka ta saba yi.

ADVERTISEMENT

Nasarar yakin duniya na biyu nasara ce ga dukkanin bil Adama, sabanin ta wata kasa daya kadai. Miyagun hasarorin da yakin ya haifar sun bayyana cewa, danniya da zalunci ba hanyar da ta dace ta cudanyar al’ummomin duniya ba ce, kuma nuna karfin soja ba dabara ce ta kiyaye zaman lafiya ba, haka kuma cin nasara daga faduwar wani bangare ba zai kai ga ci gaban dan Adam ba. Za a iya tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, matukar an yi koyi daga darasin tarihin yakin duniya na biyu, tare da yin watsi da kowane irin ra’ayi na nuna fin karfi.

Kasashen duniya na rungumar adalci a maimakon nuna fin karfi, kuma manufar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam da kasar Sin ta gabatar ta nuna mana hanyar da ta dace ta cudanyar kasashen duniya. Don haka ma, tun bayan da aka gabatar da ita a shekaru 10 da suka wuce, an shigar da ita cikin kudurin MDD, da ma tsarin kungiyar SCO da ta BRICS, lamarin da ya shaida yadda kasa da kasa suka cimma daidaito a kan wannan dabara ta kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Baya ga haka, duniya ta shaida yadda kasar Sin ta yi watsi da mulkin mallaka, da cin nasara daga faduwar wani bangare a yayin da take zamanantar da kanta, har ma ta bude sabon babin hadin gwiwar samun nasarar juna. Daga nasarorin da aka cimma bisa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, zuwa bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin da ya samar da dandalin more damammaki ga duniya, kuma daga samar da hidimomin tauraron dan Adam na Beidou ga kasa da kasa, zuwa yadda fasahar Juncao ta samar da moriya ga kasashe sama da 100, kasar Sin ta shaida wa duniya cewa, kasashe masu tasowa suna iya zamantar da kansu ba tare da bin hanyar da kasashen yamma suka bi a baya ba.

Tarihi ya haskaka makomar dan Adam, kuma muna da imanin cewa, Bil’adama zai iya samar wa kansa kyakkyawar makoma muddin ya rike tarihi a zuci, kuma ba za su kai ga cimma nasara a kan kalubalen da ke gabansu ba, har sai sun hada kai da juna. (Lubabatu)

Tarihi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Tarihi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.