• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Ƙaryata Jita-jitar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London

by Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Ƙaryata Jita-jitar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa wai an mayar da Jerin Taron Bayanin Ministoci Ga ‘Yan Jarida daga Abuja zuwa London.

 

Ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a lokacin buɗe jerin taron na takwas da aka gudanar a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
  • Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Ya ce: “Ga amsar ku ga ji-ta-ji-tar cewa wai za a mayar da taron ‘yan jarida zuwa ƙetare. Muna da nauyin da ya rataya a wuyan mu na farko ga Nijeriya, shi ya sa muke gayyatar ministoci su zo nan su yi wa ‘yan Nijeriya da ma waɗanda ke waje jawabi kai-tsaye daga nan Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

 

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

“Don haka, idan kuna tunanin cewa taron bayanin ministoci, kamar yadda wasu ke yaɗa cewa za a mayar da shi zuwa wajen ƙasar, ba gaskiya ba ne.

 

“Wannan dandamali da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai take samarwa, nan ne inda abin ke faruwa, a nan ƙasar.”

 

Taron ya samu halartar Ministar Harkokin Al’adu da Tattalin Arzikin Ƙirƙira, Hannatu Musawa; da Ministan Ruwa da Tsaftace Muhalli, Farfesa Joseph Utsev, da kuma Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi.

 

Sanata Umahi, wanda aka ruwaito ba daidai ba cewa yana daga cikin ministocin da za su gabatar da nasarorin Gwamnatin Shugaban Ƙasa Tinubu a wani taro a London, ya goyi bayan furucin Idris, yana mai cewa rahoton ba gaskiya ba ne.

 

Idris ya kuma taɓo batun tattalin arzikin ƙasa, inda ya yi nuni da Rahoton Nuna Canjin Farashin Kayayyaki (CPI) na watan Afrilu 2025 da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa ta fitar.

 

Ya ce: “Yau, ina farin cikin bayyana wani labari mai daɗi daga Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa, wadda ta fitar da Rahoton Nuna Canjin Farashin Kayayyaki (CPI) na watan Afrilu 2025, jiya. Bisa ga rahoton, adadin hauhawar farashin kayayyaki na watan Afrilu ya tsaya a kashi 23.71, wanda ke nuna ragin kashi 0.52 daga 24.23 da aka rubuta a watan Maris 2025.

 

“Haka kuma, idan aka kwatanta wata da wata, hauhawar farashin ya ragu sosai da kashi 2.04, daga 3.90 a Maris zuwa 1.86 a Afrilu.

 

“Wannan ba ya faruwa haka ziƙau. Tsare-tsaren Shugaban Ƙasa da aka mayar da hankali a kai su ne suke haifar da ɗa mai ido. Fa’idar gyare-gyaren da ake yi, ko da yake a hankali suke zuwa, tabbatattu ne kuma mutum zai iya auna su.”

 

Ya bayyana cewa hauhawar farashin kayayyakin abinci – wanda ke ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa hauhawar farashi – ya fara raguwa sakamakon tsare-tsaren Shugaban Ƙasa Tinubu.

 

Ya ce: “Ɗaya daga cikin manyan alamu na sauƙin da ake samu shi ne ƙimar hauhawar farashin abinci. Duk da cewa farashin abinci har yanzu yana damun mutane da dama a Nijeriya, hauhawar farashin abinci daga shekara zuwa shekara ya ragu zuwa kashi 21.26 a watan Afrilu.

 

“Idan aka duba wata zuwa wata kuwa, ya ragu zuwa kashi 2.06, daga kashi 2.18 da aka samu a Maris. Wannan cigaba mai kyau ya samo asali ne daga ragin farashin muhimman kayan abinci irin su garin masara, hatsi, garin doya, kuɓewa, gyaɗa, shinkafa, da wake.

 

“Jama’a, mun san cewa har yanzu ba mu kai inda muke fatar kaiwa ba. Amma waɗannan alƙaluman da aka samu kwanan nan suna ba mu cikakken dalili na yin fatan alheri. Suna nuna cewa matakan da muka ɗauka masu wahala sun fara haifar da kyakkyawan sakamako. Kuma yayin da farashi yake sauka, muna sa ran ganin sauƙi a ƙarfin sayen kayan masarufi da kuma rayuwar jama’a gaba ɗaya.”

 

Ministan ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa Gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da ɗaukar matakan da ke mayar da hankali kan rayuwar jama’a don kawo sauƙi, da dawo da daidaiton tattalin arziki, da inganta walwala ga kowa da kowa.

 

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da ba da labarin irin wannan cigaban cikin gaskiya, yana mai jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da zama mai gabatar da komai a bayyane kuma amintacciya ga ‘yan ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A 16/05/2025

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

Related

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

7 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

10 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

10 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

12 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

12 hours ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

13 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.