• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Ma'adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake ya karbi bakuncin rukuni na farko na Askarawan kare ma’adanai da aka kafa kwanan nan domin su yi aikin kare wuraren da ake hakar ma’adanai a sassan kasar nan.

An kafa Askarawan ne a karkashin jagorancin shugaban hukumar tsaron farin kaya (NSCDC), Abubakar Audi. A ranar 1 ga watan Maris ne Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ya kaddamar da rundunar don su yi aikin kawo karshen masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a sassan Nijeriya, wanda hakan ake sa ran zai inganta kudaden shiga a bangaren tattalin arzikin Nijeriya.

  • Ba Ka Da Aiki Sai Yin Barci A Abuja – Martanin Ɗan El-Rufai Ga Uba Sani
  • El-Rufai Ya Jibge Min Bashin $587 Da Biliyan 85 A Kaduna – Uba Sani

Kaddamar da dakarun ya yi daidai da bikin ranar da majalisar dinkin duniya ta ware don bikin ranar kula da hakkin fararen hula a duniya, wanda aka yi a Abuja.
Ma’aikatar ma’adanai ne ta su kula da ayyukan Askarawan.

An shirya cewa, za a tattaro dakarun ne daga jihohin tarayyar Nijeriya da babban birnin tarayya Abuja inda a halin yanzu aka kafa runduna mai mutum 60.

Alake ya umarci dakarun su tabbatar da sun kawo karshen sace-sace da ayyukan ta’addanci da ke faruwa a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Minista Alake ya kuma yaba wa Minista Olubunmi-Ojo a kan yadda ya tsayu na ganin an samu nasarar kafa rundunar.

“An kaddamar da Askarawan ne tare da hadin gwiwar ministan cikin gida don kare wuraren hakar ma’adanai, ta haka za a tabbatar da cin gajiyar albarkatun ma’adanai da Allah ya shinfida a sassan Nijeriya.Wannan kuma na daga cikin shirye-shiryen da Shugaba Tinubu ya yi na bunkasa bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya, ”Kamar yadda Segun Tomori mai ba Minista Alake shawara a kan harkokin yada labarai ya bayyana a sanarwa da ya raba wa manema labarai.

“Ina mai farin cikin sanar da al’umma cewa, an kafa dakarun ne don tsaftace wuraren hakar ma’adanai daga matsalar tsaro, mun kuma samu nasarar kafa rukuni na farko na jami’an da za su yi wannan aikin kamar yadda muka kaddamar a yau.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum
Manyan Labarai

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
Labarai

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Next Post
Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.