ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Biya Tarar Naira Miliyan 585 Domin A Saki Daurarru 4,068

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Minista

Gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar harkokin cikin gida ta biya tarar naira miliyan 585 domin a saki daurarru 4,068 da suka kasa biyan tarar da alkalai suka yanke musu a gidajen yarin Nijeriya.

Ministan harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, wanda ya kaddamar da biyan tarar a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja, ya ce an dauki wannan matakin ne da nufin rage cunkoso a gidajen yari da ke fadin kasar nan.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Japan Ta Amince Kasashen Duniya Su Sa Ido Kan Yadda Take Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Da yake jawabi a gidan yarin Kuje wanda aka saki fursunoni 37, Tunji-Ojo ya ce wannan sabuwar dabara ce na rage cunkoso a gidajen yarin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A ranar 17 ga Nuwamba, 2023, akwai kimanin fursunoni 80,804 a cikin gidajen gyaran hali da ke fadin kasar nan guda 253, wanda ya kamata a saka daurarru kasa da 50,000. Wannan ya nuna cewa akwai cunkoso a gidajen yarinmu.

“A yau, mun saki jimillar fursunoni 4,068 da ke zaman gidan yari sakamakon rashin biyan tara ko diyya.Yawancin fursunonin da suka samu ‘yancin talakawa ne da ba za su iya biyan tarar da alkalai suka yanke musu ba wanda hakan ta sa suke zaune a gidan yari.”

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Ya kara da cewa kaddamar da shirin biyan naira miliyan 585 ya ta’allaka ne da kudaden da masu hannu da shuni da kungiyoyi da hukumomi suka tara wajen tallafa wa al’umma.

Tunji-Ojo ya bayyana cewa duk fursunonin da ke gidajen yari saboda rashin biyan tara ko diyya da bai wuce naira miliyan daya ba, su sukaA ci gajiyar wannan shiri. Ya kuma bayyana cewa fursunonin da aka sako an ba su jarin da za su yi wata sana’a idan suka koma yankunansu.

Tun da farko da yake jawabi, shugaban gidan yarin, Haliru Nababa, ya siffanta wannan shirin a matsayin mai matukar muhimmanci kuma abin sha’awa. Ya jaddada himma da jajircewar minista na ci gaba da sauye-sauyen da ake yi a gidajen yarin Nijeriya.

Ya kara da cewa, wannan shiri na ma’aikatar harkokin cikin gida ya samar da wani gagarumin abun yabawa ga daidaikun mutane, kamfanoni da sauran masu ruwa da tsaki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Sojoji Da ‘Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

Sojoji Da 'Yan banga Sun Ceto Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.