• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga masu ƙirƙira da masu tasiri a shafukan sada zumunta da su rage munanan kalamai kan Nijeriya tare da fifita muradun ƙasar ta hanyar bin ƙa’idojin ɗa’a wajen gudanar da ayyukansu.

 

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a Abuja, yayin bikin Makon Ilimin Yaɗa Labarai da Bayanai na Duniya na Ƙasa na 2024 mai taken “New Digital Frontiers of Information: Media and Information Literacy for Public Interest Information” wanda Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta shirya tare da haɗin gwiwar Cibiyar Ilimin Yaɗa Labarai da Bayanai ta Duniya, Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya.

  • Arewa ta fi Talakawa, Ta Cancanci Samun Karin Tallafi Mai Yawa – Minista Mai Jiran Gado
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, Mataimaki na Musamman ga Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai ya fitar, Idris ya jaddada muhimmancin daidaita suka da kishin ƙasa, inda ya buƙaci masu ƙirƙira a shafukan sada zumunta da su yi la’akari da muradun ƙasa yayin yaɗa bayanai.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

Ya bayyana cewa, “Yana da muhimmanci mu riƙa suka da kuma sanya gwamnati da sauran shugabanni su yi bayani domin aikin kafafen yaɗa labarai kenan…Amma kuma yana da matuƙar muhimmanci a wajen bayar da rahoto, mu fifita muradin ƙasa.”

 

“Ina sake maimaitawa, ba za mu iya tsammanin girma da kuma samun mutane su zo su zuba jari a ƙasarmu ba yayin da duk abin da muke turawa waje a kowane lokaci ba shi da kyau. Akwai labarai masu kyau da yawa da ke fitowa daga Nijeriya kuma ya zama wajibi mu kasance masu kishin ƙasa yayin da muke bayar da rahoto domin Nijeriya ta kai ga inda take so ta kai na wadata da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi magana a kai,” inji shi.

 

Ministan ya yi Allah-wadai da yaɗuwar labaran ƙarya a shafukan sada zumunta, inda ya yi gargaɗin cewa, idan ba a daƙile ba, hakan na haifar da barazana ga haɗin kai, zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

 

Ya bayyana cewa, “Duk wanda ke da kwamfutar tafi-da-gidanka ko wayar android zai iya zama mai samar da labarai, wanda zai iya isa ga mutane masu yawa. Sai dai, wannan shimfiɗar wuri na dijital… yana haifar da matsaloli masu muni, musamman tare da yaɗuwar bayanan ƙarya.”

 

Idris ya yabawa UNESCO bisa ƙoƙarin da take yi na yaƙi da labaran ƙarya a Nijeriya ta hanyar kafa Cibiyar Ilimin Yaɗa Labarai da Bayanai ta Duniya.

 

Ya sanar da cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai tare da haɗin gwiwar Budaddiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN) na ci gaba da mayar da cibiyar ta zama Cibiyar UNESCO ta Rukuni na 2.

 

Wakilin UNESCO a Nijeriya, Abdourahamane Diallo, ya kuma jaddada muhimmancin shigar da Ilimin Yaɗa Labarai (MIL) cikin tsarin karatun Nijeriya.

 

Mataimakin Shugaban Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya, Farfesa Olufemi Peters, ya gode wa Ministan bisa goyon bayan da yake bai wa jami’ar wajen ƙarfafa ayyukan Cibiyar Ilimin Yaɗa Labarai da Bayanai ta Duniya da ke cikin jami’ar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yancin DimokuradiyyaKuncin rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daukakar Nasaba Da Girman Garinsa (SAW)

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

42 minutes ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

2 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

3 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

6 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

7 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.