• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Jaddada Muhimmiyar Alfanun Kafafen Yaɗa Labarai A Cikin Al’umma

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada muhimmiyar rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen jagorantar al’umma, da inganta fahimtar juna, da kuma bayar da gudunmawa ga gagarumin cigaba.

 

Idris ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da wani shirin talabijin mai taken “Traverse China With Me,” wanda na haɗin gwiwa ne tsakanin Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da kuma China Media Group (CMG) a ranar Alhamis a Cibiyar Al’adun Ƙasar Sin da ke Abuja.

  • Manoma Sun Magantu A Kan Rashin Raba Takin Zamani A Lokaci
  • Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba

A wajen taron, Idris ya bayyana cewa shirin zai ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin gidajen talabijin na Nijeriya da kafofin watsa labarai na ƙasar Sin, wato Chaina.

 

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Ya ƙara da cewa wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta alaƙa tsakanin al’ummar Nijeriya da Sin ta hanyar musayar al’adu da harshe, ta hanyar amfani da hanyoyin sadarwa na zamani da ake da su a ƙasashen biyu.

 

Ministan ya yaba wa hukumomin CMG da NTA bisa jajircewar su wajen samar da ingantattun labarai da shirye-shirye masu ma’ana waɗanda ke taimaka wa cigaban ƙasashen biyu.

 

Ya ce haɗin gwiwar zai yi tasiri mai kyau ga harkokin zamantakewa, cigaban tattalin arziki, da cigaban al’adu.

 

Idris ya kuma jaddada muhimmancin daidaita rahotanni, musamman wajen bayyana cigaban da aka samu, da kuma samar da shirye-shirye da za su haifar da kyakkyawar fatar samun cigaba a nan gaba.

 

Ya ce Nijeriya da ke da ɗimbin matasa tana fuskantar ƙalubale da dama da suka haɗa da yaɗa labaran ƙarya da ji-ta-ji-ta waɗanda ke haifar da koma-baya da rashin yarda tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasar.

 

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na Chaina da su haɗa kai da Nijeriya da sauran takwarorin su na ƙasa da ƙasa don daƙile wannan mummunar ɗabi’a da tabbatar da inganci da aminci a cikin harkar yaɗa labarai.

 

Bugu da ƙari, ministan ya yi kira ga CMG da ya faɗaɗa kafafen yaɗa labaran sa a Nijeriya ta hanyar haɗawa da wasu harsuna, kamar Hausa, Ibo, Yarbanci, da Pijin.

 

Ya ce hakan ba kawai zai inganta sadarwa ba, har ma zai samar da guraben aikin yi da horar da ‘yan Nijeriya.

 

Ita ma Daraktar Sashen Hausa na CMG, Kande Gao, ta yi jawabi a wajen taron, inda ta bayyana alaƙar da ke tsakanin Sin da Nijeriya, tare da yin kira da a ƙara yin hadin gwiwa.

 

Ta bayyana cewa kamfanin CMG ya himmatu wajen samar da fahimtar juna a tsakanin ƙasashen biyu, kamar yadda ake nunawa a cikin shirye-shirye irin su “Traverse China With Me,” wanda ya samu karɓuwa musamman a yankunan da ake magana da harshen Hausa.

 

Taron ya samu halartar wakilai daga NTA, gidan Rediyon Nijeriya, Muryar Nijeriya, da Hukumar Kula da Kafofin Yaɗa Labarai a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Nijeriya Na Bukatar Naira Tiriliyan 55 Domin Cike Gibin Gidaje A Cikin Shekara 10

Nijeriya Na Bukatar Naira Tiriliyan 55 Domin Cike Gibin Gidaje A Cikin Shekara 10

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.