ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Jaddada Muhimmiyar Alfanun Kafafen Yaɗa Labarai A Cikin Al’umma

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada muhimmiyar rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen jagorantar al’umma, da inganta fahimtar juna, da kuma bayar da gudunmawa ga gagarumin cigaba.

 

Idris ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da wani shirin talabijin mai taken “Traverse China With Me,” wanda na haɗin gwiwa ne tsakanin Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da kuma China Media Group (CMG) a ranar Alhamis a Cibiyar Al’adun Ƙasar Sin da ke Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Manoma Sun Magantu A Kan Rashin Raba Takin Zamani A Lokaci
  • Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba

A wajen taron, Idris ya bayyana cewa shirin zai ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin gidajen talabijin na Nijeriya da kafofin watsa labarai na ƙasar Sin, wato Chaina.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya ƙara da cewa wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta alaƙa tsakanin al’ummar Nijeriya da Sin ta hanyar musayar al’adu da harshe, ta hanyar amfani da hanyoyin sadarwa na zamani da ake da su a ƙasashen biyu.

 

Ministan ya yaba wa hukumomin CMG da NTA bisa jajircewar su wajen samar da ingantattun labarai da shirye-shirye masu ma’ana waɗanda ke taimaka wa cigaban ƙasashen biyu.

 

Ya ce haɗin gwiwar zai yi tasiri mai kyau ga harkokin zamantakewa, cigaban tattalin arziki, da cigaban al’adu.

 

Idris ya kuma jaddada muhimmancin daidaita rahotanni, musamman wajen bayyana cigaban da aka samu, da kuma samar da shirye-shirye da za su haifar da kyakkyawar fatar samun cigaba a nan gaba.

 

Ya ce Nijeriya da ke da ɗimbin matasa tana fuskantar ƙalubale da dama da suka haɗa da yaɗa labaran ƙarya da ji-ta-ji-ta waɗanda ke haifar da koma-baya da rashin yarda tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasar.

 

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na Chaina da su haɗa kai da Nijeriya da sauran takwarorin su na ƙasa da ƙasa don daƙile wannan mummunar ɗabi’a da tabbatar da inganci da aminci a cikin harkar yaɗa labarai.

 

Bugu da ƙari, ministan ya yi kira ga CMG da ya faɗaɗa kafafen yaɗa labaran sa a Nijeriya ta hanyar haɗawa da wasu harsuna, kamar Hausa, Ibo, Yarbanci, da Pijin.

 

Ya ce hakan ba kawai zai inganta sadarwa ba, har ma zai samar da guraben aikin yi da horar da ‘yan Nijeriya.

 

Ita ma Daraktar Sashen Hausa na CMG, Kande Gao, ta yi jawabi a wajen taron, inda ta bayyana alaƙar da ke tsakanin Sin da Nijeriya, tare da yin kira da a ƙara yin hadin gwiwa.

 

Ta bayyana cewa kamfanin CMG ya himmatu wajen samar da fahimtar juna a tsakanin ƙasashen biyu, kamar yadda ake nunawa a cikin shirye-shirye irin su “Traverse China With Me,” wanda ya samu karɓuwa musamman a yankunan da ake magana da harshen Hausa.

 

Taron ya samu halartar wakilai daga NTA, gidan Rediyon Nijeriya, Muryar Nijeriya, da Hukumar Kula da Kafofin Yaɗa Labarai a Nijeriya.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Nijeriya Na Bukatar Naira Tiriliyan 55 Domin Cike Gibin Gidaje A Cikin Shekara 10

Nijeriya Na Bukatar Naira Tiriliyan 55 Domin Cike Gibin Gidaje A Cikin Shekara 10

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.