ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Jaddada Muhimmiyar Alfanun Kafafen Yaɗa Labarai A Cikin Al’umma

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada muhimmiyar rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen jagorantar al’umma, da inganta fahimtar juna, da kuma bayar da gudunmawa ga gagarumin cigaba.

 

Idris ya bayyana hakan ne a yayin ƙaddamar da wani shirin talabijin mai taken “Traverse China With Me,” wanda na haɗin gwiwa ne tsakanin Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA) da kuma China Media Group (CMG) a ranar Alhamis a Cibiyar Al’adun Ƙasar Sin da ke Abuja.

ADVERTISEMENT
  • Manoma Sun Magantu A Kan Rashin Raba Takin Zamani A Lokaci
  • Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba

A wajen taron, Idris ya bayyana cewa shirin zai ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin gidajen talabijin na Nijeriya da kafofin watsa labarai na ƙasar Sin, wato Chaina.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ƙara da cewa wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta alaƙa tsakanin al’ummar Nijeriya da Sin ta hanyar musayar al’adu da harshe, ta hanyar amfani da hanyoyin sadarwa na zamani da ake da su a ƙasashen biyu.

 

Ministan ya yaba wa hukumomin CMG da NTA bisa jajircewar su wajen samar da ingantattun labarai da shirye-shirye masu ma’ana waɗanda ke taimaka wa cigaban ƙasashen biyu.

 

Ya ce haɗin gwiwar zai yi tasiri mai kyau ga harkokin zamantakewa, cigaban tattalin arziki, da cigaban al’adu.

 

Idris ya kuma jaddada muhimmancin daidaita rahotanni, musamman wajen bayyana cigaban da aka samu, da kuma samar da shirye-shirye da za su haifar da kyakkyawar fatar samun cigaba a nan gaba.

 

Ya ce Nijeriya da ke da ɗimbin matasa tana fuskantar ƙalubale da dama da suka haɗa da yaɗa labaran ƙarya da ji-ta-ji-ta waɗanda ke haifar da koma-baya da rashin yarda tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasar.

 

Ya buƙaci kafafen yaɗa labarai na Chaina da su haɗa kai da Nijeriya da sauran takwarorin su na ƙasa da ƙasa don daƙile wannan mummunar ɗabi’a da tabbatar da inganci da aminci a cikin harkar yaɗa labarai.

 

Bugu da ƙari, ministan ya yi kira ga CMG da ya faɗaɗa kafafen yaɗa labaran sa a Nijeriya ta hanyar haɗawa da wasu harsuna, kamar Hausa, Ibo, Yarbanci, da Pijin.

 

Ya ce hakan ba kawai zai inganta sadarwa ba, har ma zai samar da guraben aikin yi da horar da ‘yan Nijeriya.

 

Ita ma Daraktar Sashen Hausa na CMG, Kande Gao, ta yi jawabi a wajen taron, inda ta bayyana alaƙar da ke tsakanin Sin da Nijeriya, tare da yin kira da a ƙara yin hadin gwiwa.

 

Ta bayyana cewa kamfanin CMG ya himmatu wajen samar da fahimtar juna a tsakanin ƙasashen biyu, kamar yadda ake nunawa a cikin shirye-shirye irin su “Traverse China With Me,” wanda ya samu karɓuwa musamman a yankunan da ake magana da harshen Hausa.

 

Taron ya samu halartar wakilai daga NTA, gidan Rediyon Nijeriya, Muryar Nijeriya, da Hukumar Kula da Kafofin Yaɗa Labarai a Nijeriya.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Nijeriya Na Bukatar Naira Tiriliyan 55 Domin Cike Gibin Gidaje A Cikin Shekara 10

Nijeriya Na Bukatar Naira Tiriliyan 55 Domin Cike Gibin Gidaje A Cikin Shekara 10

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.