• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya roƙi kamfanin taskace bayanai a intanet (Google), da ya daƙile bazuwar dukkan saƙwannin da ka iya zama haɗari da barazana ga ɗorewar dunƙulalliyar al’umma a ƙasa ɗaya.

Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar manyan jami’an Google na Afrika ta Yamma, bisa jagorancin daraktansu, Mista Olumide Balogun.

  • CMG Ya Kaddamar Da Bikin Baje Kolin “Hanyar Samun Wayewar Kai” A London
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Tara Min Kudi Don Yi Wa Tinubu Waka Saboda Kaunarsa -Mawaki Rarara

Tawagar ta kai masa ziyara ne a ranar Alhamis, a Abuja.

Ya ce: “Akwai matuƙar muhimmanci a ga cewa an tantance tasiri da kuma illolin manhajojin yaɗa bayanai ta intanet. Ina ganin ku ne aikin hana yaɗuwar abu mai illa ya fi wajaba a kan ku.

“Gwamnati ba ta da aniya ko tunanin ƙaƙaba wa ‘yancin faɗar albarkacin baki ko ‘yan jarida takunkumi. Shugaban Ƙasa ba mai so ya ga ana tauye ‘yancin faɗar albarkacin baki ba ne.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

“To sai dai kuma, idan har aka ce bayani mai haɗari ne, zai iya zama babbar matsala kenan a gare mu. Zai tarwatsa haɗin kanmu tare da haifar mana da ruɗu a cikin ƙasa.

“Mun san cewa isar da saƙwannin bayanai ta intanet na da muhimmanci sosai wajen ɗorewar ƙasa har ta tsaya da diddiginta a matsayin ƙasa. Don haka akwai buƙatar samun ‘yancin bayyana ra’ayi a kafar da kowa zai ji ba a tauye masa haƙƙi ko ‘yanci ba.

“Saboda haka, muddin aka samu fahimta ta hanyar isar da sakonnin bayanai a cikin jama’a, to za a rage ɗarɗar da ambaliyar labarai na bogi. A kula, ‘yanci ya na tafiya ne tare da sanin ƙa’idoji da ya kamata.”

Minista ya ƙara da cewa, Google na da gagarumin haƙƙi na ganin cewa haƙƙin da aka bai wa mutane su na watsa bayanai a kafafen sada zumunta bai zama musabbabin haifar da hargitsi ga ‘yan Nijeriya ba.

Da ya ke nasa jawabin tun da farko, Mista Balogun ya shaida wa ministan cewa, cikin shekaru uku da su ka gabata zuwa yanzu kamfanin ya horas da ‘yan jarida 3,500 a Nijeriya.

Ya ce an horas da su ne dabarun amfani da hanyoyin fasahar zamani wajen tantance sahihan labarai, da tace labaran bogi da sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GoogleMinistan Yaɗa LabaraiMuhammad Idris
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Zuba Jarin Dala Miliyan 617 A Fannin Fasahar Sadarwa

Next Post

Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

1 hour ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

3 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

4 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

7 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

8 hours ago
Next Post
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.