• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi Google Ta Dakatar Da Yada Labarai Masu Barazana Ga Hadin Kan Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Google

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya roƙi kamfanin taskace bayanai a intanet (Google), da ya daƙile bazuwar dukkan saƙwannin da ka iya zama haɗari da barazana ga ɗorewar dunƙulalliyar al’umma a ƙasa ɗaya.

Ministan ya yi wannan kira ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar manyan jami’an Google na Afrika ta Yamma, bisa jagorancin daraktansu, Mista Olumide Balogun.

  • CMG Ya Kaddamar Da Bikin Baje Kolin “Hanyar Samun Wayewar Kai” A London
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Tara Min Kudi Don Yi Wa Tinubu Waka Saboda Kaunarsa -Mawaki Rarara

Tawagar ta kai masa ziyara ne a ranar Alhamis, a Abuja.

Ya ce: “Akwai matuƙar muhimmanci a ga cewa an tantance tasiri da kuma illolin manhajojin yaɗa bayanai ta intanet. Ina ganin ku ne aikin hana yaɗuwar abu mai illa ya fi wajaba a kan ku.

“Gwamnati ba ta da aniya ko tunanin ƙaƙaba wa ‘yancin faɗar albarkacin baki ko ‘yan jarida takunkumi. Shugaban Ƙasa ba mai so ya ga ana tauye ‘yancin faɗar albarkacin baki ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

“To sai dai kuma, idan har aka ce bayani mai haɗari ne, zai iya zama babbar matsala kenan a gare mu. Zai tarwatsa haɗin kanmu tare da haifar mana da ruɗu a cikin ƙasa.

“Mun san cewa isar da saƙwannin bayanai ta intanet na da muhimmanci sosai wajen ɗorewar ƙasa har ta tsaya da diddiginta a matsayin ƙasa. Don haka akwai buƙatar samun ‘yancin bayyana ra’ayi a kafar da kowa zai ji ba a tauye masa haƙƙi ko ‘yanci ba.

“Saboda haka, muddin aka samu fahimta ta hanyar isar da sakonnin bayanai a cikin jama’a, to za a rage ɗarɗar da ambaliyar labarai na bogi. A kula, ‘yanci ya na tafiya ne tare da sanin ƙa’idoji da ya kamata.”

Minista ya ƙara da cewa, Google na da gagarumin haƙƙi na ganin cewa haƙƙin da aka bai wa mutane su na watsa bayanai a kafafen sada zumunta bai zama musabbabin haifar da hargitsi ga ‘yan Nijeriya ba.

Da ya ke nasa jawabin tun da farko, Mista Balogun ya shaida wa ministan cewa, cikin shekaru uku da su ka gabata zuwa yanzu kamfanin ya horas da ‘yan jarida 3,500 a Nijeriya.

Ya ce an horas da su ne dabarun amfani da hanyoyin fasahar zamani wajen tantance sahihan labarai, da tace labaran bogi da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.