• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ayyuka Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara Kan Ayyukan Sabunta Birane

by Leadership Hausa
2 years ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samu yabo daga Ministan Ayyuka, David Umahi, bisa gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu a ayyukan sabunta birane.

A ranar Juma’ar ce Ministan ya kai ziyarar aiki Jihar Zamfara a wani rangadin da yake yi na duba ayyukan titunan Gwamnatin Tarayya a jihar.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce ministan ya duba ayyukan titunan Gwamnatin Tarayya da ke gudana wanda ya kai tsawon kilomita 277.305, daga Zariya zuwa Sheme, Sheme zuwa Gusau, da Gusau zuwa Mafara.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan da muƙarrabansa sun lura da ɗumbin nasarorin da aka samu a aikin sabunta biranen da gwamnatin Gwamna Lawal ke gudanarwa.

  • Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

 

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yaba wa ministan bisa yunƙurinsa na duba ayyukan manyan titunan Gwamnatin Tarayya.

“Ina tabbatar muku da cewa akwai alheri domin akan bayar da kwangilar gina tituna, amma babu wanda ke zuwa dubawa daga Gwamnatin Tarayya. Zuwar ku na da matuƙar amfani..

“Minista, kamar yadda ka tabbatar, ba a daina faɗaɗa hanyoyi ba, kamar yadda ake ta yayatawa. Wannan labari ne mai daɗi.

“Ina so in nuna godiyata da kyawawan kalamanka. A matsayinmu na gwamnati mai kishin ƙasa, muna aiki tuƙuru don ganin mun canja mummunan yanayin Jihar Zamfara. A da, duk lokacin da ka ji labarin Jihar Zamfara, a kan yi tunanin abu mara kyau ne. Amma yanzu muna ƙoƙarin ceto da sake gina jihar.

“Ina kuma son in yi godiya ga shugaban ƙasa bisa ga ƙoƙarin da ya yi na aiwatar da muhimman ayyukan Gwamnatin Tarayya. Za mu ci gaba da goyon bayan kyawawan manufofinsa.”

A jawabinsa, ministan ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne umarci a yi rangaɗin domin ganin yadda ayyukan ke gudana.

“Gwamna, mun zo nan ne bisa umarnin shugaban ƙasa domin duba ayyukan tituna da ke gudana tare da isar da gaisuwarsa gare ku.

“Shugaban ƙasa ya ƙuduri aniyar kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa, da suka haɗa da faɗaɗa titunan tarayya, ba a Zamfara kaɗai ba har ma a faɗin ƙasar nan baki ɗaya.

“Ina yaba muku kan ƙoƙorin ku na ci gaba da aiwatar da ayyukan sabunta birane da suka kawo sauyi a Zamfara cikin watanni tara kacal.”

Shugaban kwamitin Majalisar Dattijai mai kula da gidaje da tituna, Aminu Waziri Tambuwal, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato yana cikin tawagar ministan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.