ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ayyuka Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara Kan Ayyukan Sabunta Birane

by Leadership Hausa
2 years ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samu yabo daga Ministan Ayyuka, David Umahi, bisa gagarumin ci gaban da gwamnatinsa ta samu a ayyukan sabunta birane.

A ranar Juma’ar ce Ministan ya kai ziyarar aiki Jihar Zamfara a wani rangadin da yake yi na duba ayyukan titunan Gwamnatin Tarayya a jihar.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce ministan ya duba ayyukan titunan Gwamnatin Tarayya da ke gudana wanda ya kai tsawon kilomita 277.305, daga Zariya zuwa Sheme, Sheme zuwa Gusau, da Gusau zuwa Mafara.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan da muƙarrabansa sun lura da ɗumbin nasarorin da aka samu a aikin sabunta biranen da gwamnatin Gwamna Lawal ke gudanarwa.

  • Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

 

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yaba wa ministan bisa yunƙurinsa na duba ayyukan manyan titunan Gwamnatin Tarayya.

“Ina tabbatar muku da cewa akwai alheri domin akan bayar da kwangilar gina tituna, amma babu wanda ke zuwa dubawa daga Gwamnatin Tarayya. Zuwar ku na da matuƙar amfani..

“Minista, kamar yadda ka tabbatar, ba a daina faɗaɗa hanyoyi ba, kamar yadda ake ta yayatawa. Wannan labari ne mai daɗi.

“Ina so in nuna godiyata da kyawawan kalamanka. A matsayinmu na gwamnati mai kishin ƙasa, muna aiki tuƙuru don ganin mun canja mummunan yanayin Jihar Zamfara. A da, duk lokacin da ka ji labarin Jihar Zamfara, a kan yi tunanin abu mara kyau ne. Amma yanzu muna ƙoƙarin ceto da sake gina jihar.

“Ina kuma son in yi godiya ga shugaban ƙasa bisa ga ƙoƙarin da ya yi na aiwatar da muhimman ayyukan Gwamnatin Tarayya. Za mu ci gaba da goyon bayan kyawawan manufofinsa.”

A jawabinsa, ministan ayyuka, David Umahi, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne umarci a yi rangaɗin domin ganin yadda ayyukan ke gudana.

“Gwamna, mun zo nan ne bisa umarnin shugaban ƙasa domin duba ayyukan tituna da ke gudana tare da isar da gaisuwarsa gare ku.

“Shugaban ƙasa ya ƙuduri aniyar kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa, da suka haɗa da faɗaɗa titunan tarayya, ba a Zamfara kaɗai ba har ma a faɗin ƙasar nan baki ɗaya.

“Ina yaba muku kan ƙoƙorin ku na ci gaba da aiwatar da ayyukan sabunta birane da suka kawo sauyi a Zamfara cikin watanni tara kacal.”

Shugaban kwamitin Majalisar Dattijai mai kula da gidaje da tituna, Aminu Waziri Tambuwal, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato yana cikin tawagar ministan.

zamfara
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

Buhari Ya Haddasa Wa Nijeriya Koma-baya Na Tsawon Shekara 50 — Fayose

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.