• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 

by Hussein Yero and Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Ministan Tsaro Ya Jinjina Wa Gwamnan Zamfara, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen ‘Yan Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da bayar da goyon baya ga ayyukan soji a jihar.

 

A ranar Alhamis ɗin nan ne ministan ya ziyarci gidan gwamnatin Zamfara da hedikwatar rundunar haɗin gwiwa ta ‘Operation Fansar Yamma’ da ke Gusau.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran
  • TCN Ta Gano Dalilin Katsewar Wutar Lantarki A Arewacin Nijeriya, Ta Fara Gyara

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ziyarar na da nufin inganta haɗin gwiwa tsakanin jihar da ma’aikatar tsaro.

 

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sanarwar ta ƙara da cewa, ministan ya tattauna batutuwan da suka shafi ziyarar da gwamna Lawal da gwamna Raɗɗa suka kai Ma’aikatar Tsaro a farkon makon nan.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na bayar da haɗin kai ga dukkanin hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Zamfara.

 

“Ina so in miƙa godiyata ga Ministan Tsaro, wanda ya zo yau domin tattauna batun matsalar tsaro a Zamfara.

 

“Kwanaki kaɗan da suka gabata ni da gwamnan jihar Katsina muka je ofishin minista a Ma’aikatar Tsaro, inda muka tattauna batutuwa masu muhimmanci.

 

“Bayan kwana biyu, ministan ya zo wurinmu. Wannan abin a yaba ne na irin ƙwazon da ministan ya nuna.

 

“Zamfara na fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, amma a matsayinmu na gwamnati mai cikakken iko, duk mun tashi tsaye don neman taimako da haɗa kai da hukumomin tsaro. Mun himmatu wajen ba da dukan taimako ga sojoji.

 

“Za mu kai yaƙi ne ga ‘yan bindigar saboda kare kanmu. Abin da na gani zuwa yanzu ya nuna cewa batun ‘yan bindiga zai zama tarihi in Allah Ya yarda.

 

“Na yi alƙawari ga ministan. Bugu da ƙari, na saya wa sojoji motocin da harsashi ba ya fasa su guda goma. Haka kuma akwai sauran kayan aikin da za a ba jami’an tsaro domin taimaka musu wajen yaƙar ‘yan bindiga.

 

“Idan za mu iya magance ƙalubalen ‘yan bindiga a Zamfara, za a magance kashi 90 na matsalar jihar.

 

“Ina kira ga jami’an tsaro, musamman sojoji, cewa muna buƙatar su. Ina da yaƙinin suna da abin da ake buƙata don kawar da ‘yan ta’adda.

 

“Na yi alƙawari, kuma ina tare da ku. Ina godiya ga kowa da kowa, musamman Minista da ke ba da lokacin zama tare da mu.”

 

A farko dai, Ministan Tsaro, Alhaji Badaru Abubakar, ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ‘yan bindiga na da alaƙa da ci gaba da goyon bayan gwamnatin Gwamna Lawal.

 

“Mun fara ganin an samu ci gaba, sakamakon goyon bayan Gwamnan Jihar Zamfara.

 

“Gwamnan ya samar da masauki ga kwamandojin soji, wuraren horo, kyamarori masu sa ido na nesa, motoci, da dai sairan kayan aiki. Har ma ya bai wa sojojin motocin yaƙi. Ranka ya daɗe, mun gode maka sosai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Masar Da Iran

Next Post

Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

3 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

4 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

5 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

9 hours ago
Next Post
Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

Fashewar Tankar Mai A Jigawa: Remi Tinubu Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan ₦40m Da Kayayyakin Abinci

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.