• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Tsokaci Kan Yanayin Da Ake Ciki A Shiyyoyi Daban Daban

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Tsokaci Kan Yanayin Da Ake Ciki A Shiyyoyi Daban Daban
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Lahadi, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a wasu shiyyoyi daban daban, a wani taron manema labaru da ya gudana a birnin Alkahira na kasar Masar, bayan da ya gana da takwaransa na kasar Masar Sameh Shoukry.

Dangane da rikicin da ake fama da shi a zirin Gaza, ministan na kasar Sin ya ce, rikicin na ta kara tsanani, lamarin da ya haddasa rasa rayukan dimbin fararen hula, da haifar da mummunan tasiri ga karin yankuna makwabta cikin matukar sauri. A cewar jami’in, kasar Sin a ko da yaushe tana goyon bayan ra’ayi mai dauke da adalci, inda take kokarin neman ganin a tsagaita bude wuta, a hadin gwiwarta da kasashen Larabawa, da na Musulmi, don kare fararen hula, da neman samun damar daidaita batun Falasdinu cikin adalci kuma daga tushe tun da wuri.

  • CMG Ta Kammala Bitar Farko Ta Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Bana
  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan

Sa’an nan, game da maganar tsaro da ta shafi bahar Maliya, jami’in Sin ya ce, kasar Sin tana damuwa da mai da cikakken hankali kan batun. Kana kasar ta yi kira da a dakatar da kai hari ga jiragen ruwa na fararen hula, don kare tsarin samar da kayayyaki da na cinikayya a duniya. A cewar Malam Wang, dalilin da ya sa ake samun tashin hankali a yankin bahar Maliya, shi ne habakar rikici daga zirin Gaza zuwa sauran wurare. Yanzu aikin da ya kamata a aiwatar da shi cikin gaggawa shi ne, a kwantar da kurar da ta tashi a Gaza, don magance ci gaban bazuwar rikicin.

Ban da haka, jami’in ya yi tsokaci kan yanayin da ake ciki a yankin Taiwan na kasar Sin. Ya ce, zaben da aka yi a yankin, aikin cikin gida ne na kasar Sin. Kana duk wani sakamakon da aka samu wajen zaben, ba zai canza hakikanin yanayin da ake ciki ba, wato kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, kana Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Kana ba zai girgiza ra’ayi na bai daya da gamayyar kasa da kasa ke da shi na kasancewar kasar Sin guda daya kawai ba.

Bugu da kari, Mr. Wang Yi wanda yake kai ziyara kasar Tunisia, ya bayyana sabon kwalejin nazarin harkokin diflomasiyyar kasa da kasa na Tunis, wato kwaleji daya tilo na harkokin diflomasiyya da aka kaddamar a yau Litinin, kuma Sin ta taimaka wajen ginawa a wata kasar Larabawa, a matsayin sabuwar alama ta dankon zumunta, kuma dandalin raya abotar Sin da Tunisia.

Labarai Masu Nasaba

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Wang Yi ya bayyana haka ne yau, lokacin da yake jawabi yayin bikin bude kwalejin a birnin Tunis. Bikin ya samu halartar shugaban kasar, Kais Saied da ministan harkokin wajen kasar, Nabil Ammar.

Wang Yi ya kuma yi kira da a yi kokarin inganta gina tsarin duniya mai daidaito tsakanin kasashen duniya da dama da dunkulewar tattalin arzikin duniya domin kowa ya amfana. (Bello Wang, Fa’iza Mustapha)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashe Da Dama Na Adawa Da Yunkurin Ware Taiwan Daga Babban Yankin Kasar Sin

Next Post

Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 – WHO

Related

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

57 minutes ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

4 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

5 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

6 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

18 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

22 hours ago
Next Post
Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 – WHO

Muna Bukatar Dala Biliyan 1 Don Ceto Rayuka A 2024 - WHO

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.