• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan ma’aikatar harkokin wajen tarayyar Najeriya Yusuf Maitama Tuggar, ya ce karkashin manufofin kasar Sin da suka hada da dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, da shawarar ziri daya da hanya daya, Sin ta samarwa kasashen Afirka ciki har da Najeriya, wasu damammakin samar da ci gaba na musamman.

Tuggar, wanda ya bayyana hakan yayin zantawa da ‘yan jaridar kafar CMG a kwanan baya, lokacin da yake ziyarar aiki a kasar Sin, ya ce Najeriya na aiki tukuru wajen ingiza hadin gwiwa da Sin a fannoni daban daban, wadanda suka hada da raya layukan dogo, da hanyoyin mota, da bututan iskar gas da lantarki. Ya ce Sin ta zuba jari mai tarin yawa a fannin gina ababen more rayuwa, wanda hakan ya ingiza damar samar da guraben ayyukan yi ga ‘yan Najeriya, kuma hakan ya yi matukar amfanar kasar.

  • Kasar Sin Ta Amince Da Dokar Ba Da Agajin Gaggawa Da Aka Yi Wa Kwaskwarima
  • Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

Ministan ya kara da cewa, nahiyar Afirka na bukatar karin jari mai tarin yawa, domin bunkasa fitar da hajojin da aka sarrafa a cikin nahiyar, ba wai kawai kayan da ake fitarwa domin a sarrafa a waje ba. Kuma kasar Sin ta tabbatar da kudurin ta na taimakwa wajen warware wadannan matsaloli, ta kuma nuna matukar goyon bayan ta ga Afirka, ta hanyar juba jari mai yawa a nahiyar.

Ya ce bisa yadda kamfanonin Sin ke shiga ana damawa da su, sashen sarrafa batiran lithium na Najeriya na kara fadada. Kaza lika hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin sabbin makamashi, zai fadada cin gajiya daga sassan daban daban masu nasaba, ciki har da na kirar ababen hawa masu aiki da lantarki. Kuma baya ga kasuwar cikin gida ta Najeriya, fannin zai kuma samar da hajojin fitarwa zuwa sauran kasashen duniya. Hadin gwiwar sassan biyu zai samar da muhimmin tallafi ga Najeriya a fannin raya masana’antun ta.

Game da batun fasahar kirkirarriyar basira ko AI kuwa, ministan ya ce Najeriya na da matasa masu hazaka, da za su taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da hadin gwiwa da Sin a fannin na AI. Don haka ya yi fatan cewa, kasashen biyu za su fadada hadin gwiwa a fannonin musayar al’adu, da ilimi, da harkokin zamantakewa, da horaswa a fannin samar kwarewa. Mista Tuggar ya kara da cewa, Sin ba ta kallon duniya ta fuskar taswirar yankuna, maimakon haka, tana fatan dunkulewa karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, ta yadda kasashe da yankunan duniya za su kara kusantar juna. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴan Ta’addan Da Suka Kai Hari Borno Zasu Yabawa Aya Zaƙinta – Tinubu

Next Post

Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Related

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye
Daga Birnin Sin

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

1 hour ago
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

19 hours ago
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

20 hours ago
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

21 hours ago
Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo
Daga Birnin Sin

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

23 hours ago
Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani

24 hours ago
Next Post
Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Jami'ar Yar'adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa - ASUU

LABARAI MASU NASABA

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

August 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

August 20, 2025
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

August 20, 2025
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.