• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan ma’aikatar harkokin wajen tarayyar Najeriya Yusuf Maitama Tuggar, ya ce karkashin manufofin kasar Sin da suka hada da dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, da shawarar ziri daya da hanya daya, Sin ta samarwa kasashen Afirka ciki har da Najeriya, wasu damammakin samar da ci gaba na musamman.

Tuggar, wanda ya bayyana hakan yayin zantawa da ‘yan jaridar kafar CMG a kwanan baya, lokacin da yake ziyarar aiki a kasar Sin, ya ce Najeriya na aiki tukuru wajen ingiza hadin gwiwa da Sin a fannoni daban daban, wadanda suka hada da raya layukan dogo, da hanyoyin mota, da bututan iskar gas da lantarki. Ya ce Sin ta zuba jari mai tarin yawa a fannin gina ababen more rayuwa, wanda hakan ya ingiza damar samar da guraben ayyukan yi ga ‘yan Najeriya, kuma hakan ya yi matukar amfanar kasar.

  • Kasar Sin Ta Amince Da Dokar Ba Da Agajin Gaggawa Da Aka Yi Wa Kwaskwarima
  • Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

Ministan ya kara da cewa, nahiyar Afirka na bukatar karin jari mai tarin yawa, domin bunkasa fitar da hajojin da aka sarrafa a cikin nahiyar, ba wai kawai kayan da ake fitarwa domin a sarrafa a waje ba. Kuma kasar Sin ta tabbatar da kudurin ta na taimakwa wajen warware wadannan matsaloli, ta kuma nuna matukar goyon bayan ta ga Afirka, ta hanyar juba jari mai yawa a nahiyar.

Ya ce bisa yadda kamfanonin Sin ke shiga ana damawa da su, sashen sarrafa batiran lithium na Najeriya na kara fadada. Kaza lika hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin sabbin makamashi, zai fadada cin gajiya daga sassan daban daban masu nasaba, ciki har da na kirar ababen hawa masu aiki da lantarki. Kuma baya ga kasuwar cikin gida ta Najeriya, fannin zai kuma samar da hajojin fitarwa zuwa sauran kasashen duniya. Hadin gwiwar sassan biyu zai samar da muhimmin tallafi ga Najeriya a fannin raya masana’antun ta.

Game da batun fasahar kirkirarriyar basira ko AI kuwa, ministan ya ce Najeriya na da matasa masu hazaka, da za su taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da hadin gwiwa da Sin a fannin na AI. Don haka ya yi fatan cewa, kasashen biyu za su fadada hadin gwiwa a fannonin musayar al’adu, da ilimi, da harkokin zamantakewa, da horaswa a fannin samar kwarewa. Mista Tuggar ya kara da cewa, Sin ba ta kallon duniya ta fuskar taswirar yankuna, maimakon haka, tana fatan dunkulewa karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, ta yadda kasashe da yankunan duniya za su kara kusantar juna. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴan Ta’addan Da Suka Kai Hari Borno Zasu Yabawa Aya Zaƙinta – Tinubu

Next Post

Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Related

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

12 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

13 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

14 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

15 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

16 hours ago
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

17 hours ago
Next Post
Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Jami'ar Yar'adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.