ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Rangers

Kawo yanzu dai kungiyar kwallon kafa ta Enugu Rangers ta lashe kofin babbar gasar firimiyar Nijeriya a karo na takwas bayan doke kungiyar kwallon kafa ta Gombe United har gida da ci 2-1.

Rangers ta samu jimillar maki 70 a gasar ta Nijeriya Professional Footbal League (NPFL) kakar wasa ta 2023 zuwa 2024, wanda hakan ke nufin ta samu tikitin zuwa gasar Zakarun Afirka na shekara mai zuwa.

  • Barazanar Da Rashin Katabus Na Kananan Hukumomi Ke Yi Ga Dimokuradiyyar Nijeriya
  • Yadda Aka Yi Bikin Kaddamar Da Littafin Babban Editan LEADERSHIP A Abuja

An gudanar da bikin ba ta kofin ne a filin wasa na Jos International Stadium – inda Gombe United ke buga wasanninta na gida kuma bayan wasannin mako na 38 kamar yadda yake a doka.

ADVERTISEMENT

Kungiyar Rangers ce ta fara cin kwallo minti uku da fara wasa ta hannun dan wasa Ogunleye, sannan Obaje ya kara minti hudu bayan haka, kafin Hassan ya farke wa Gombe kwallo daya a minti na 25.

Tun a ranar 16 ga watan Mayu Rangers ta hada maki 67 a saman teburi da ya ba ta zama gwarzuwar gasar bayan doke Bendel Insurance 2-0, sai dai kafin lashe gasar, Rangers ta ci wasanni 21 cikin 38 da ta buga, ta yi canjaras bakwai sannan ta yi rashin nasara sau 10.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Remo Stars ce ta kare a mataki na biyu da maki 65, sai kuma kungiyar Enyimba a mataki na uku da maki 63, wadanda suka samu gurbin shiga gasar zakarun Afirka ta badi.

Kamar yadda aka saba, kungiyoyi hudu na kasan teburi ne ke sauka daga babba zuwa karamar gasar ta firimiya wato Nijeriya National League (NNL). kungiyoyin su ne Sporting Lagos, Doma United, Heartland da kuma Gombe United.

Wasannin da aka buga a ranar Lahadi ne suka tabbatar da an kammala gasar kuma an buga jimillar wasanni 370, cikin kungiyoyi 20 da suka fafata tsawon kakar wasa daya kuma ita ce karo na 52 a tarihi.

 

Ga wasu abubuwa 10 da suka faru a gasar:

1. Dan wasan Enyimba, Bictor Mbaoma, shi ne kan gaba wajen jefa kwallaye a raga bayan ya ci kwallaye 16 a wasannin da ya fafata. 2. Dan wasan gaba na Kano Pillars, Yusuf Abdullahi, shi ne kadai ya ci kwallo sama da uku a wasa daya – inda ya ci Gombe United kwallo biyar a wasan da suka yi nasara 5-2 a kakar.

3 . ‘Yan wasa shida ne kacal suka ci kwallo uku rigis a wasa daya a kakar da aka kammala, su ne Robert Mizo (Bayelsa United), Yusuf Abdullahi (Kano Pillars) da dan wasa Albert Hillary (Plateau United), Nyima Nwagua (Ribers United), Silas Nenrot (Plateau United), Ubong Friday (Akwa United) da kuma Godwin Obaje (Plateau United).

4. Remo Stars ce ta fi kowacce kungiya karbar jan kati a kakar bana, inda aka bai wa ‘yan wasanta jan katin har sau bakwai – Enyimba ce ke biye mata da shida. 5 – Tun ana saura wasa daya a gama gasar Rangers ta dauki kofin wanda ba a fiya samun haka ba.

6. Doma United da ta sauka daga gasar, ta fi kowa buga wasa mai yawa ba tare da an zira mata kwallo a raga ba – da guda uku kawai ta dara zakarun gasar, wato kungiyar Rangers.

7 – Rangers sun fi kowa buga wasa mai yawa ba tare da rashin nasara ba, inda ta jera wasa 10 ba a doke ta ba – ta dara Doma United da wasa daya. 8 – Heartland wadda ta sauka daga gasar – ita ce ta fi kowa yawan wasa a jere ba tare da nasara ba. Ta buga wasa 11 babu nasara, sai kuma Doma da Gombe da suka buga 10-10 a jere babu nasara.

9 – Dan wasan Plateau United, Silas Nenrot, shi ne ya ci kwallo uku rigis a mafi kankantar lokaci a bana. Dan wasan gaban ya ci cikin minti 11 a wasan da suka doke Gombe United 4-0 a wasan mako 25.

10 – An ba da jan kati sau 49. 11 – An buga finareti 90, inda aka ci 70 kuma aka barar da 20.

12 – An ci kwallaye 848. 13 – Sau 29 kungiyoyoyi suka yi nasara a wasannin da suka buga a waje. 14 – Gombe ce ta fi kowa dibar kwallaye, inda aka zira mata 76 jimilla.

15 – An buga canjaras a wasa 86.

Rangers
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.