ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Rangers

Kawo yanzu dai kungiyar kwallon kafa ta Enugu Rangers ta lashe kofin babbar gasar firimiyar Nijeriya a karo na takwas bayan doke kungiyar kwallon kafa ta Gombe United har gida da ci 2-1.

Rangers ta samu jimillar maki 70 a gasar ta Nijeriya Professional Footbal League (NPFL) kakar wasa ta 2023 zuwa 2024, wanda hakan ke nufin ta samu tikitin zuwa gasar Zakarun Afirka na shekara mai zuwa.

  • Barazanar Da Rashin Katabus Na Kananan Hukumomi Ke Yi Ga Dimokuradiyyar Nijeriya
  • Yadda Aka Yi Bikin Kaddamar Da Littafin Babban Editan LEADERSHIP A Abuja

An gudanar da bikin ba ta kofin ne a filin wasa na Jos International Stadium – inda Gombe United ke buga wasanninta na gida kuma bayan wasannin mako na 38 kamar yadda yake a doka.

ADVERTISEMENT

Kungiyar Rangers ce ta fara cin kwallo minti uku da fara wasa ta hannun dan wasa Ogunleye, sannan Obaje ya kara minti hudu bayan haka, kafin Hassan ya farke wa Gombe kwallo daya a minti na 25.

Tun a ranar 16 ga watan Mayu Rangers ta hada maki 67 a saman teburi da ya ba ta zama gwarzuwar gasar bayan doke Bendel Insurance 2-0, sai dai kafin lashe gasar, Rangers ta ci wasanni 21 cikin 38 da ta buga, ta yi canjaras bakwai sannan ta yi rashin nasara sau 10.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Remo Stars ce ta kare a mataki na biyu da maki 65, sai kuma kungiyar Enyimba a mataki na uku da maki 63, wadanda suka samu gurbin shiga gasar zakarun Afirka ta badi.

Kamar yadda aka saba, kungiyoyi hudu na kasan teburi ne ke sauka daga babba zuwa karamar gasar ta firimiya wato Nijeriya National League (NNL). kungiyoyin su ne Sporting Lagos, Doma United, Heartland da kuma Gombe United.

Wasannin da aka buga a ranar Lahadi ne suka tabbatar da an kammala gasar kuma an buga jimillar wasanni 370, cikin kungiyoyi 20 da suka fafata tsawon kakar wasa daya kuma ita ce karo na 52 a tarihi.

 

Ga wasu abubuwa 10 da suka faru a gasar:

1. Dan wasan Enyimba, Bictor Mbaoma, shi ne kan gaba wajen jefa kwallaye a raga bayan ya ci kwallaye 16 a wasannin da ya fafata. 2. Dan wasan gaba na Kano Pillars, Yusuf Abdullahi, shi ne kadai ya ci kwallo sama da uku a wasa daya – inda ya ci Gombe United kwallo biyar a wasan da suka yi nasara 5-2 a kakar.

3 . ‘Yan wasa shida ne kacal suka ci kwallo uku rigis a wasa daya a kakar da aka kammala, su ne Robert Mizo (Bayelsa United), Yusuf Abdullahi (Kano Pillars) da dan wasa Albert Hillary (Plateau United), Nyima Nwagua (Ribers United), Silas Nenrot (Plateau United), Ubong Friday (Akwa United) da kuma Godwin Obaje (Plateau United).

4. Remo Stars ce ta fi kowacce kungiya karbar jan kati a kakar bana, inda aka bai wa ‘yan wasanta jan katin har sau bakwai – Enyimba ce ke biye mata da shida. 5 – Tun ana saura wasa daya a gama gasar Rangers ta dauki kofin wanda ba a fiya samun haka ba.

6. Doma United da ta sauka daga gasar, ta fi kowa buga wasa mai yawa ba tare da an zira mata kwallo a raga ba – da guda uku kawai ta dara zakarun gasar, wato kungiyar Rangers.

7 – Rangers sun fi kowa buga wasa mai yawa ba tare da rashin nasara ba, inda ta jera wasa 10 ba a doke ta ba – ta dara Doma United da wasa daya. 8 – Heartland wadda ta sauka daga gasar – ita ce ta fi kowa yawan wasa a jere ba tare da nasara ba. Ta buga wasa 11 babu nasara, sai kuma Doma da Gombe da suka buga 10-10 a jere babu nasara.

9 – Dan wasan Plateau United, Silas Nenrot, shi ne ya ci kwallo uku rigis a mafi kankantar lokaci a bana. Dan wasan gaban ya ci cikin minti 11 a wasan da suka doke Gombe United 4-0 a wasan mako 25.

10 – An ba da jan kati sau 49. 11 – An buga finareti 90, inda aka ci 70 kuma aka barar da 20.

12 – An ci kwallaye 848. 13 – Sau 29 kungiyoyoyi suka yi nasara a wasannin da suka buga a waje. 14 – Gombe ce ta fi kowa dibar kwallaye, inda aka zira mata 76 jimilla.

15 – An buga canjaras a wasa 86.

Rangers
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.