ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Ministan ma’aikatar harkokin wajen tarayyar Najeriya Yusuf Maitama Tuggar, ya ce karkashin manufofin kasar Sin da suka hada da dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, da shawarar ziri daya da hanya daya, Sin ta samarwa kasashen Afirka ciki har da Najeriya, wasu damammakin samar da ci gaba na musamman.

Tuggar, wanda ya bayyana hakan yayin zantawa da ‘yan jaridar kafar CMG a kwanan baya, lokacin da yake ziyarar aiki a kasar Sin, ya ce Najeriya na aiki tukuru wajen ingiza hadin gwiwa da Sin a fannoni daban daban, wadanda suka hada da raya layukan dogo, da hanyoyin mota, da bututan iskar gas da lantarki. Ya ce Sin ta zuba jari mai tarin yawa a fannin gina ababen more rayuwa, wanda hakan ya ingiza damar samar da guraben ayyukan yi ga ‘yan Najeriya, kuma hakan ya yi matukar amfanar kasar.

  • Kasar Sin Ta Amince Da Dokar Ba Da Agajin Gaggawa Da Aka Yi Wa Kwaskwarima
  • Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

Ministan ya kara da cewa, nahiyar Afirka na bukatar karin jari mai tarin yawa, domin bunkasa fitar da hajojin da aka sarrafa a cikin nahiyar, ba wai kawai kayan da ake fitarwa domin a sarrafa a waje ba. Kuma kasar Sin ta tabbatar da kudurin ta na taimakwa wajen warware wadannan matsaloli, ta kuma nuna matukar goyon bayan ta ga Afirka, ta hanyar juba jari mai yawa a nahiyar.

ADVERTISEMENT

Ya ce bisa yadda kamfanonin Sin ke shiga ana damawa da su, sashen sarrafa batiran lithium na Najeriya na kara fadada. Kaza lika hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin sabbin makamashi, zai fadada cin gajiya daga sassan daban daban masu nasaba, ciki har da na kirar ababen hawa masu aiki da lantarki. Kuma baya ga kasuwar cikin gida ta Najeriya, fannin zai kuma samar da hajojin fitarwa zuwa sauran kasashen duniya. Hadin gwiwar sassan biyu zai samar da muhimmin tallafi ga Najeriya a fannin raya masana’antun ta.

Game da batun fasahar kirkirarriyar basira ko AI kuwa, ministan ya ce Najeriya na da matasa masu hazaka, da za su taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da hadin gwiwa da Sin a fannin na AI. Don haka ya yi fatan cewa, kasashen biyu za su fadada hadin gwiwa a fannonin musayar al’adu, da ilimi, da harkokin zamantakewa, da horaswa a fannin samar kwarewa. Mista Tuggar ya kara da cewa, Sin ba ta kallon duniya ta fuskar taswirar yankuna, maimakon haka, tana fatan dunkulewa karkashin shawarar ziri daya da hanya daya, ta yadda kasashe da yankunan duniya za su kara kusantar juna. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Jami’ar Yar’adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa – ASUU

Jami'ar Yar'adua Da Ke Katsina Ta Kama Hanyar Durƙushewa - ASUU

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.