• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kaddamar Da Shafin Kundin Bayanan Nijeriya Na Yanar Gizo 

by Sulaiman
1 year ago
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da shafin kundin yada labarai da bayar da bayanai na Gwamnatin Nijeriya a matsayin wata babbar hanyar sadarwa ta zamani don samun cikakkun bayanai game da ƙasar.

Idris, wanda ya ƙaddamar da shafin a lokacin da aka fara gabatar da bayanai na Ayyukan Ministoci don bikin cikar gwamnatin Tinubu shekara ɗaya, ya ce gidan yanar wata cibiya ce da aka ware domin mutanen cikin gida da na ƙasashen waje, don samar da sababbi kuma amintattun bayanai kan abubuwa daban-daban na al’amuran ƙasa da suka haɗa da gwamnati, al’ummar Nijeriya, al’adun su da dai sauran su.

  • Wata Sabuwa: Wani Alkali Daga Amurka YA Dakatar Da Sake Nada Sarki Sanusi II
  • Bukatar Lalubo Hanyoyin Cin Gajiyar Ma’adinai A Nijeriya

Ya ce: “Muna amfani da wannan damar wajen ƙaddamar da shafin kundin labarai na yanar gizo na Yaɗa Labarai na Nijeriya. Tabbas, akwai shi a baya amma ba a kula da shi da kyau ba har Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta sake farfaɗo da wannan sabon shafin.

“Hanya ce ga duk bayanan da kuke buƙatar sani game da wannan gwamnati; game da Nijeriya, mutane, da al’adun mu. Don haka, mu gode wa gwamnatin Nijeriya da ta sake buɗe wannan sabon gidan yanar yaɗa labarai na ƙasa.”

Shafin shi ne kamar haka: www.nigeria.gov.ng.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

Tun da fari da yake gabatar da jawabin buɗe taron, ministan ya ce Shugaban Ƙasa ya soma kafa ginshiƙi mai nagarta kuma mai ɗorewa wanda zai inganta rayuwar jama’ar Nijeriya.

Ya ce: “Manyan shirye-shirye irin su Hukumar Bada Lamuni ga Masu Sayayya, Gidauniyar Lamunin Ilimi ta Nijeriya, Shirin Shugaban Ƙasa na Samar da Iskar Gas, Shirin Shugaban Ƙasa na Bada Lamuni na Naira Biliyan
200, ƙoƙarin mu na Aikin Goma da Ba da Tsaro domin Samar da Abinci (wanda ya haɗa da ƙaddamar da Noman Rani, da gagarumin aikin raba takin zamani), Shirin Haɓaka Wuraren Ayyuka na Sabuwar Fata, (RHIDF), Shirin Birane da Gidaje na Sabuwar Fata, ayyukan mu na yin gyara a Fannin Wutar Lantarki, da kuma ɓangaren Tsarin Haraji da Hada-hadar Kuɗi, da tattaunawar da ake yi na za a samar da albashi mafi ƙaranci na ƙasa, – suna daga cikin manyan tsare-tsare da shirye-shirye masu yawa waɗanda kai-tsaye za su shafi rayuwa da hanyoyin samun kuɗin shiga kuma su inganta rayuwa da abincin miliyoyin ‘yan Nijeriya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Matatar dangote
Labarai

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Labarai

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Next Post
Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga

Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Labarai

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.