• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kaddamar Da Shafin Kundin Bayanan Nijeriya Na Yanar Gizo 

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Ministan Yaɗa Labarai Ya Kaddamar Da Shafin Kundin Bayanan Nijeriya Na Yanar Gizo 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da shafin kundin yada labarai da bayar da bayanai na Gwamnatin Nijeriya a matsayin wata babbar hanyar sadarwa ta zamani don samun cikakkun bayanai game da ƙasar.

Idris, wanda ya ƙaddamar da shafin a lokacin da aka fara gabatar da bayanai na Ayyukan Ministoci don bikin cikar gwamnatin Tinubu shekara ɗaya, ya ce gidan yanar wata cibiya ce da aka ware domin mutanen cikin gida da na ƙasashen waje, don samar da sababbi kuma amintattun bayanai kan abubuwa daban-daban na al’amuran ƙasa da suka haɗa da gwamnati, al’ummar Nijeriya, al’adun su da dai sauran su.

  • Wata Sabuwa: Wani Alkali Daga Amurka YA Dakatar Da Sake Nada Sarki Sanusi II
  • Bukatar Lalubo Hanyoyin Cin Gajiyar Ma’adinai A Nijeriya

Ya ce: “Muna amfani da wannan damar wajen ƙaddamar da shafin kundin labarai na yanar gizo na Yaɗa Labarai na Nijeriya. Tabbas, akwai shi a baya amma ba a kula da shi da kyau ba har Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta sake farfaɗo da wannan sabon shafin.

“Hanya ce ga duk bayanan da kuke buƙatar sani game da wannan gwamnati; game da Nijeriya, mutane, da al’adun mu. Don haka, mu gode wa gwamnatin Nijeriya da ta sake buɗe wannan sabon gidan yanar yaɗa labarai na ƙasa.”

Shafin shi ne kamar haka: www.nigeria.gov.ng.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Tun da fari da yake gabatar da jawabin buɗe taron, ministan ya ce Shugaban Ƙasa ya soma kafa ginshiƙi mai nagarta kuma mai ɗorewa wanda zai inganta rayuwar jama’ar Nijeriya.

Ya ce: “Manyan shirye-shirye irin su Hukumar Bada Lamuni ga Masu Sayayya, Gidauniyar Lamunin Ilimi ta Nijeriya, Shirin Shugaban Ƙasa na Samar da Iskar Gas, Shirin Shugaban Ƙasa na Bada Lamuni na Naira Biliyan
200, ƙoƙarin mu na Aikin Goma da Ba da Tsaro domin Samar da Abinci (wanda ya haɗa da ƙaddamar da Noman Rani, da gagarumin aikin raba takin zamani), Shirin Haɓaka Wuraren Ayyuka na Sabuwar Fata, (RHIDF), Shirin Birane da Gidaje na Sabuwar Fata, ayyukan mu na yin gyara a Fannin Wutar Lantarki, da kuma ɓangaren Tsarin Haraji da Hada-hadar Kuɗi, da tattaunawar da ake yi na za a samar da albashi mafi ƙaranci na ƙasa, – suna daga cikin manyan tsare-tsare da shirye-shirye masu yawa waɗanda kai-tsaye za su shafi rayuwa da hanyoyin samun kuɗin shiga kuma su inganta rayuwa da abincin miliyoyin ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamnatin NijeriyaShafin yada labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-Yanzu: Sarki Sunusi Ya Isa Gidan Gwamnatin Kano

Next Post

Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Labarai
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga

Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.