• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta tsaro da bayar da ƙarin tallafi ga dakarun da ke yaƙi da ’yan bindiga a Zamfara.

A ranar Alhamis ne gwamnan ya jagoranci zaman Majalisar Tsaro ta Jihar Zamfara a fadar gwamnati da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an tattauna muhimman batutuwa kan matsalar tsaro a jihar da kuma hare-haren da ’yan bindiga ke kaiwa.

  • Wata Sabuwa: Wani Alkali Daga Amurka YA Dakatar Da Sake Nada Sarki Sanusi II

 

A cewarsa, taron ya samu halartar dukkan shugabannin hukumomin tsaro na jihar da suka haɗa da sojoji, ’yansanda, DSS, da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Yayin da yake jawabi ga shugabannin hukumomin tsaro, Gwamna Lawal ya yaba wa sojojin bisa nasarorin da aka samu kawo yanzu a yaƙin da ake yi da ’yan ta’adda.

“Taron na yau zai duba yanayin matsalar tsaro da jihar ke fama da shi, da kuma tantance irin ci gaban da muka samu, da kuma tantance wuraren da ke buƙatar ƙara ƙaimi wajen inganta tsaron rayuka da dukiyoyin jama’armu.

“Kamar yadda na sha nanata wa majalisar tsaro a ko da yaushe, fifikon gwamnatina shi ne tsaron rayuka da dukiyoyi. Don haka a ko da yaushe a shirye muke mu bayar da dukkan goyon bayan da ya kamata ga hukumomin tsaro daban-daban na jihar domin taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

“Ina so in gode wa Gwamnatin Tarayya da sojoji saboda tura ƙarin dakaru zuwa Zamfara. Wannan mataki na nufin kawar da duk ‘yan bindiga, kuma mun fara ganin sakamako.

“Na kuma yaba da nasarar cafke gungun masu garkuwa da mutane a Gusau tare da kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su a faɗin jihar da suka haɗa da Gusau, Maradun, Kauran Namoda, da sauran ƙananan hukumomin. Waɗannan nasarorin da aka samu shaida ce da ke nuna tasirin ayyukan soji da ake yi a jihar.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Dauda LawalTsaroYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kaddamar Da Shafin Kundin Bayanan Nijeriya Na Yanar Gizo 

Next Post

Ganawar Tsoffin Gwamnonin Zamfara Ta Siyasa Ce Ba Tsaro Ba – Gwamnan Jihar

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

2 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

10 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

12 hours ago
Next Post
zamfara

Ganawar Tsoffin Gwamnonin Zamfara Ta Siyasa Ce Ba Tsaro Ba – Gwamnan Jihar

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.