ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Tsaron Jihar Zamfara Ta Tantance Nasarorin Da Ake Samu Kan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga

by Leadership Hausa
2 years ago
tsaro

Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta tsaro da bayar da ƙarin tallafi ga dakarun da ke yaƙi da ’yan bindiga a Zamfara.

A ranar Alhamis ne gwamnan ya jagoranci zaman Majalisar Tsaro ta Jihar Zamfara a fadar gwamnati da ke Gusau, babban birnin jihar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa an tattauna muhimman batutuwa kan matsalar tsaro a jihar da kuma hare-haren da ’yan bindiga ke kaiwa.

ADVERTISEMENT
  • Wata Sabuwa: Wani Alkali Daga Amurka YA Dakatar Da Sake Nada Sarki Sanusi II

 

A cewarsa, taron ya samu halartar dukkan shugabannin hukumomin tsaro na jihar da suka haɗa da sojoji, ’yansanda, DSS, da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Yayin da yake jawabi ga shugabannin hukumomin tsaro, Gwamna Lawal ya yaba wa sojojin bisa nasarorin da aka samu kawo yanzu a yaƙin da ake yi da ’yan ta’adda.

“Taron na yau zai duba yanayin matsalar tsaro da jihar ke fama da shi, da kuma tantance irin ci gaban da muka samu, da kuma tantance wuraren da ke buƙatar ƙara ƙaimi wajen inganta tsaron rayuka da dukiyoyin jama’armu.

“Kamar yadda na sha nanata wa majalisar tsaro a ko da yaushe, fifikon gwamnatina shi ne tsaron rayuka da dukiyoyi. Don haka a ko da yaushe a shirye muke mu bayar da dukkan goyon bayan da ya kamata ga hukumomin tsaro daban-daban na jihar domin taimaka musu wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

“Ina so in gode wa Gwamnatin Tarayya da sojoji saboda tura ƙarin dakaru zuwa Zamfara. Wannan mataki na nufin kawar da duk ‘yan bindiga, kuma mun fara ganin sakamako.

“Na kuma yaba da nasarar cafke gungun masu garkuwa da mutane a Gusau tare da kuɓutar da waɗanda aka yi garkuwa da su a faɗin jihar da suka haɗa da Gusau, Maradun, Kauran Namoda, da sauran ƙananan hukumomin. Waɗannan nasarorin da aka samu shaida ce da ke nuna tasirin ayyukan soji da ake yi a jihar.”

tsaro
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
zamfara

Ganawar Tsoffin Gwamnonin Zamfara Ta Siyasa Ce Ba Tsaro Ba – Gwamnan Jihar

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.