• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Masanin Aikin Jarida, Kabir Ɗangogo

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Alhinin Rasuwar Fitaccen Masanin Aikin Jarida, Kabir Ɗangogo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana jimami kan rasuwar gogaggen ɗan jaridar nan, Malam Kabir Ɗangogo, wanda ƙwararren masanin aikin hulɗa da jama’a ne da aka ba lambobin yabo.

 

Haka kuma shi ne tsohon Sakatare-Janar na Ƙungiyar Aikin Hulɗa da Jama’a ta Afirka (African Public Relations Association, APRA).

  • Kwallon Mata: Nijeriya Ta Nuna Wa Afrika Ta Kudu Kwanji A Pretoria
  • Kasar Sin Za Ta Kara Albarkatu Da Kudade Domin Tallafawa Samar Da Ayyukan Yi

Malam Kabir Ɗangogo dai ya rasu ne a Kaduna a ranar Juma’a da ta gabata, yana da shekaru 76. An yi jana’izar sa a Masallacin Sarkin Musulmi Bello bayan sallar Juma’a kafin a kai shi gidan sa na gaskiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

An haife shi a ranar 21 ga Fabrairu, 1949, kuma ya yi karatu a Jami’ar Ohio da ke Athens a Amurka, a 1981, da Jami’ar Leicester ta ƙasar Birtaniya a 1987.

 

Ya yi aiki a kamfanin jaridun New Nigerian, da hukumar talbijin ta NTA, da Ofishin Yaɗa Labarai na Amurka (USIS). Haka kuma ya yi koyarwa a Kaduna Polytechnic, ya yi aiki a Bankin Arewa da kuma Bankin Union inda a nan ya yi ritaya a ranar 26 ga Yuni, 2005.

 

A cikin saƙon ta’aziyyar sa a ranar Asabar, Minista Idris ya bayyana rasuwar Malam Kabir Ɗangogo a matsayin babban rashi ga Nijeriya da fannin sadarwa a nahiyar Afirka.

 

Ya ce: “Mutuwa ta ƙwace mana ƙwararren ma’aikaci wanda ke da cikakkiyar sadaukarwa ga aiki, da ƙwarewa a aikin jarida, da kuma gagarumar gudunmawar da ya bayar a fannin hulɗa da jama’a.

 

“Ta hanyar aikin sa, ya ɗaga martabar hulɗa da jama’a a Afirka, inda ya jagoranci ci gaba da tabbatar da ɗa’a, horar da ƙwararru, da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashe.”

 

Ministan ya yaba wa Ɗangogo a matsayin jagora, mai hangen nesa, kuma uba ga masu aikin hulɗa da jama’a (wato public relations), wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta fannin a Nijeriya da Afrika baki ɗaya.

 

Ya ƙara da cewa a lokacin da Ɗangogo ke riƙe da muƙamin Sakatare-Janar na APRA, ya jajirce wajen ƙarfafa tattaunawa, da fito da sababbin abubuwa, da kuma ci gaba da tabbatar da ɗa’a a ɓangaren sadarwa da kula da suna.

 

Ya ce: “A madadin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, ina miƙa ta’aziyya ta ga iyalan sa, abokan aikin sa, da ɗaukacin ‘yan jarida da masu hulɗa da jama’a.

 

“Ina roƙon Allah ya gafarta masa, ya jiƙan sa, ya kuma ba iyalan sa haƙurin jure wannan babban rashi.”

 

Ministan ya kammala da cewa gagarumar gudunmawar da Ɗangogo ya bayar za ta ci gaba da zaburar da sababbin ‘yan jarida da masu aikin hulɗa da jama’a nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwallon Mata: Nijeriya Ta Nuna Wa Afrika Ta Kudu Kwanji A Pretoria

Next Post

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

16 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

4 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

5 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

17 hours ago
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.