Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da wasu takwarorinsa na kasashen Afirka da suka zo kasar domin halartar taron ministocin da ke kula da aiwatar da sakamakon taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) a birnin Changsha, babban birnin lardin Hunan na tsakiyar kasar Sin, a jiya Laraba.
Ministocin harkokin wajen na Afirka da aka yi ganawar da su sun hada da: Yusuf Maitama Tuggar na Nijeriya, da Bakary Yaou Sangare na Nijar, da Jean-Claude Gakosso na Jamhuriyar Congo, da Ronald Lamola na Afirka ta Kudu, da Abdoulkader Houssein Omar na Djibouti, da Samuel Okudzeto Ablakwa na Ghana, da Therese Kayikwamba Wagner ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo. Sauran su ne: Carlos Pinto Pereira na Guinea-Bissau, da Karamoko Jean-Marie Traore na Burkina Faso, da kuma Gedion Timothewos na Habasha.
Yayin ganawarsa da Tuggar, Wang ya ce, dangantakar da ke tsakanin Sin da Nijeriya na kara yin kyakkyawan tasiri a duniya bisa manyan tsare-tsare na shugabannin kasashen biyu, inda ya kara da cewa, kasar Sin na da muradin bai wa Nijeriya damarmaki na samun ci gaba.
A nasa bangaren, Tuggar ya yaba da kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da kasar Sin, inda ya bayyana aniyar kara zurfafa hadin gwiwa tare da Sin a fannoni daban daban don ciyar da alakarsu ta kawance zuwa gaba a bisa manyan tsare-tsare.
Yayin ganawarsa da Sangare kuwa, Wang ya bayyana cewa, zumuncin Sin da Nijar wani bangare ne na hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, kuma kasar Sin tana son ci gaba da sada asalin zumuncin da ke tsakanin kasashen biyu, da kara amincewa da juna. Wang ya kuma bayyana fatan kasar Nijar za ta tabbatar da tsaro da kare hakkoki da muradun kamfanonin kasar Sin da kuma Sinawa da ke kasar ta Nijar.
Da yake nasa jawabin, Sangare ya ce, Nijar na bin manufar Sin daya tak a duniya, kuma tana ba da fifiko ga hadin gwiwarta da kasar Sin, da mayar da hankali sosai kan harkokin tsaro, kana tana son kara amincewa da juna, da ci gaba da yin shawarwari bisa mutunta juna a tsakaninsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp