A yau Juma’a, ministan tsaron kasar Sin janar Dong Jun ya gana da takwaransa na kasar Amurka Lloyd Austin a yayin taron tattaunawa na Shangri-la da ake gudanarwa a kasar Singapore.
A kuma yau din, kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian ya yi bayani game da ganawar, yayin taron manema labaru da aka gudanar a kasar Singapore, inda ya ce ministocin biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan huldar dake tsakanin Sin da Amurka, da yankin Taiwan, da kuma tekun kudancin kasar Sin. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp