ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sana’o’i Bakwai Da Suka Fi Kawo Kudi A Nijeriya

by Sani Anwar
2 years ago
Nijeriya

A wannan zamani da muke ciki, akwai wasu manyan sana’o’i bakwai da ake ganin sun fi taimakawa wajen saurin kawo wa mutane kudi a Nijeriya, wadannan kuwa su ne kamar haka:

Cinikin Gidaje
Sana’ar cinikin gidaje, na daya daga cikin manyan hanyoyin samun kudadade cikin sauki, musamman a wannan kasa da muke ciki. Domin kuwa, za ka iya sayen gida ka bayar da shi haya ko kuma sayen fili ka gina; daga bisani kuma ka sayar.

Wannan ne yasa wasu ke ganin babu abin da ya kai wannan sana’a tabbas da kuma samun kudaden shiga, sakamakon tsananin bukatar da ake da ita a bangaren matsuguni a daidai wannan lokaci, musamman ganin yadda gidajen haya ke matukar wahala; sakamakon rashin gina gidajen da ba a yi yanzu, saboda tsadar kayan gini da sauran makamantansu.

ADVERTISEMENT

Noma
Babu shakka, bangaren harkokin noma a Nijeriya na ci gaba da habaka da kuma bunkasa. Wannan dalili ne yasa ake kara samun damammaki a wannan bangare da kuma samun bunkasuwar arziki.
Don haka, duk mai bukatar hanyoyin samun kudade masu yawan gaske; wajibi ne ya gaggauta rungumar wannan hanya ta noma a Nijeriya.

Kamfanin Makamashin Hasken Rana
Har ila yau, sanya hannun jari ko kafa kamfanin samar da makamashi ta hanyar hasken rana (Solar Farm), na daya daga cikin kasuwancin da yake matukar taimaka wa mutane a daidai wannan lokaci, wajen samun arziki ko kudade masu dimbin yawa a wannan zamani da muke ciki.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Kafa wannan kamfani ta hanyar amfani da makamashin hasken rana, na taimakawa wajen samar da hasken wutar lantarki tare da rarraba ta; ta hanyar sayar wa da masu bukata a samu kudi nan take.
Shakka babu, wannan hanya ce wadda a halin yanzu; musamman ganin yadda wutar lantarki ke matukar wahalar samuwa, mutane da dama sun raja’a wajen mayar da hankali; domin amfani da wannan makamashi, don samun wutar lantarki; wanda hakan ke matukar taimaka wa masu wannan sana’a wajen samun kudade masu yawan gaske.

Harkokin Cinikayya
Kasuwanci, wanda ya kunshi saye da sayar da abubuwa kamar man fetir, gwal ko zinare da kuma kayayyakin amfanin gona; na da matukar riba, amma na bukatar sani tare da fahimtar harkokin yadda ya kamata da kuma juriya.

Har ila yau, wannan kasuwanci na matukar garawa a wannan kasa tare da bayar da damar samun makudan kudade ga wadanda ke aiwatar da sana’ar.

Shi yasa duk wanda ka ga yana aiwatar da wannan kasuwanci na sayar da zinare ko sayar da mai, ba karamin attajiri ba ne, saboda sana’a ce mai matukar bukatar da isasshen jari.

Sayen Hannun Jari
A wannan gaba, sanya hannun jari; wata hanya ce da take da tabbas, sakamakon kulawa da gwamnati ta bai wa harkar tar da rage barazanar yiwuwar samun asara a cikinta. Sannan, ana kayyade adadin yawan abin da za a samu bayan tsawon wani lokaci da aka diba wa harkar.

Shi yasa, mutane da dama ke kutsawa cikin wannan kasuwa; ba tare da wani jin tsoro ba, ganin yadda harkar ke kawo kudi tare kuma da karancin yiwuwar tafka asara a cikinta.

‘Yan Nijeriya da dama, na aiwatar da wannan kasuwanci tare da samun makudan kudade lokaci bayan lokaci a fadin wannan kasa da muke ciki a saukake.

Kudaden Da Kwararru Ke Sarrafawa
A nan, wata kasuwa ce da wasu kwararru ke sarrafa nau’o’in kudade daban-daban, dangane da yadda kasuwar hada-hadar kudaden ke juyawa. Sannan, wannan kasuwanci; baya bukatar mai aiwatar da shi ya rika zurfafa bincike a cikinsa.

Manajojin asusun, su ne ke yin wannan bincike tare da tafiyar maka da hada-hadar kasuwancin, kai kana zaune abinka. Kazalika, abin da kawai kai ake bukata a wajenka shi ne; zuba wannan hannun jari a cikin kudaden da ake hada-hadarsu tare da duba ribar da kake samu ta yau da kullum.

Ajiyar Kudi Zuwa Wani Kayyadadden Lokaci
wannan na daya daga cikin hanyoyi masu sauki na samun kudi a huce da sunan kasuwanci. Abin da kawai ake nema a nan shi ne, mai sha’awar wannan kasuwanci; ya zuba jarinsa a kamfani, sannan ba zai waige shi ba; har sai bayan wa’adin lokacin da aka diba ya cika.

Babu shakka, wannan kasuwanci na da matukar riba; sannan kuma babu asara ko kadan a cikinsa, domin kuwa za a iya samun ribar da ba a taba tsammani ba; kamar yadda tsarin kasuwancin yake.

nijeriya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Ministocin Tsaron Sin Da Amurka Sun Gana A Kasar Singapore

Ministocin Tsaron Sin Da Amurka Sun Gana A Kasar Singapore

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.