• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Wasanni
0
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Morocco (FRMF) ta shigar da takardar ƙorafi a hukumance zuwa hukumar ƙwallon ƙafa ta Afrika (CAF), tana zargin “rashin adalci daga alƙalin wasa” a wasan ƙarshe na gasar cin kofin mata ta Afrika (WAFCON) da aka fafata tsakaninta da Super Falcons ta Nijeriya.

Kamar yadda jaridar Morocco World News ta ruwaito, FRMF ta bayyana cewa alƙaliyar wasan ta fasa bayar da hukuncin bugun daga kai sai mai tsaron gida (penalty) a minti na 82 da wasan ke 2-2, wanda suka ce ya kamata a baiwa tawagar su.

  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Bidiyon da aka sake dubawa ya nuna yiwuwar cewa ƴar wasan baya ta Nijeriya, Tosin Demehin, ta taɓa ƙwallo da hannu, amma bayan nazarin na’urar VAR, alƙaliyar ta soke hukuncin farko da ta yanke. Wannan mataki ya fusata ‘yan wasan Morocco da masu horas da su, inda suka ce hakan ya shafi sakamakon wasan da Nijeriya ta samu nasara da ci 3-2.

Kocin Morocco, Jorge Vilda, wanda ya jagoranci ƙasar Spain zuwa nasara a gasar cin kofin duniya ta mata a 2023, ya bayyana cewa: “Ƙaramin kuskure ne ya sa muka rasa wasan.” Duk da cewa bai saba magana kan alƙalanci ba, Vilda ya amince cewa gajiya ta taka rawa a durƙusar da tawagarsa a zagaye na biyu.

A nasa ɓangaren, kocin Nijeriya, Justine Madugu, ya yabawa Morocco bisa ƙoƙarin da suka nuna a rabin lokacin farko, yana mai cewa sauye-sauyen da suka yi a rabin lokaci na biyu ne suka sauya akalar wasan.

Labarai Masu Nasaba

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

A cewarsa: “Canje-canjen sun taka muhimmiyar rawa.” An buga wasan ƙarshe a filin wasa na Rabat Olympic Stadium, inda Morocco ta fara da ci 2-0, amma Nijeriya ta dawo da ƙwallaye daga Esther Okoronkwo, Folashade Ijamilusi, da ƴar canji Jennifer Echegini. Wannan nasara ta baiwa Super Falcons nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10 – mafi yawa a tarihin gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MoroccoSuper Falcons
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

Next Post

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Related

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

8 hours ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

2 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

3 days ago
Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku
Wasanni

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

4 days ago
Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad
Wasanni

Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

5 days ago
Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta
Wasanni

Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

5 days ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

October 3, 2025
Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.