• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kafafen yaɗa labarai wani babban ginshiƙi ne na haɓaka muhalli tare da kare martabar mulkin dimokiraɗiyya.

Ministan ya faɗi haka ne a lokacin bikin ba shi lambar yabo a wani ɓangare na Ranar ‘Yancin Aikin Jarida wanda aka yi a Abuja.

  • Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar
  • An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) ita ce ta karrama shi da lambar.

A jawabin sa jim kaɗan bayan ya karɓi lambar, Idris ya bayyana farin ciki da karramawar, musamman ganin ayyukan da ya yi da muƙaman da ya riƙe a fagen aikin jarida kafin a naɗa shi minista.

Ya ce: “Wannan karramawa ta yi min sosai, wanda ke da muhimmanci a kai na da kuma gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

“Wannan kyakkyawan karimcin zai zaburar da ni na sake sadaukar da kai ga hidimar al’ummar mu mai girma da kuma bil’adama baki ɗaya.”

Da yake magana kan taken bana na Ranar ‘Yancin Aikin Jarida, wato “Jarida ta Duniya: Aikin Jarida a Yayin da ake Fuskantar Matsalar Muhalli,” sai ministan ya ce, “A yayin da ake fuskantar matsalar muhalli, ’yan jarida sun kasance masu kula da gaskiya da kuma masu fafutikar tabbatar da gaskiya. Suna ƙarin haske kan rashin adalci na muhalli, suna fallasa ayyukan da ba daidai ba, da kuma ɗaga muryar waɗanda lalacewar muhalli ta fi shafa. Ta hanyar rahoton binciken su, suna ɗaukar gwamnatoci da ƙungiyoyin kamfanoni alhakin ayyukan su da bayar da shawarar manufofin da ke haɓaka ɗorewa da kiyaye duniyar mu.

“Taken taron na bana ya yi tasiri sosai kan manufofin ma’aikatar mu da kuma batutuwan da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sa a gaba, waɗanda suka haɗa da maido da amana, sake daidaita ƙimar ƙasa, da samar da yanayi mai kyau ga kafafen yaɗa labarai. Ya jaddada muhimmancin aikin jarida wajen magance matsalar muhalli.”

Ya ƙara da cewa, “A cikin tarihi, kafofin watsa labarai, a matsayin masu kula da gaskiya kuma masu samar da sauyi na zamantakewa, sun yi tsayin daka don yin la’akari, suna shawagi a kan ayyukan mutane, gwamnatoci, da kamfanoni.

“A wannan lokaci na rikicin muhalli, aikin watsa labarai ya wuce bayar da rahoto kawai; ya na ƙunshe ne da sadaukar da kai don shirya ayyukan gama-gari don amfanin jama’a. Tare da ikon faɗakarwa, ilmantarwa, da zaburarwa, kafofin watsa labarai su na da ikon da ba zai misaltu ba don kunna motsi, ɗaukaka muryoyi, da haifar da canjin ɗabi’a ga muhalli.”

Bugu da ƙari, Idris ya ce, “Yayin da mu ke bikin Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, dole ne mu yi tunani a kan muhimmancin kafafen watsa labarai masu ‘yanci don bunƙasa mulkin dimokiraɗiyya, inganta gaskiya, da kuma kare haƙƙin bil’adama.

“Aikin jarida ya zama ginshiƙin tsarin dimokiraɗiyya ta hanyar samar da muhimmin dandali na yaɗa labarai, musayar ra’ayi, da kuma ɗora wa masu riƙe da madafun iko alhakin su.

“Kafafen yaɗa labarai na Nijeriya sun kasance masu fafutikar tabbatar da ɗorewar mulkin dimokiraɗiyya a ƙasar nan, kuma a irin wannan lokaci, mu na jinjina wa jajircewa da sadaukarwar ku kan aikin jarida.

“Duk da haka, yayin da mu ke murnar gudunmawar da ‘yan jarida ke bayarwa ga al’umma, mun kuma yarda da ƙalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta wajen gudanar da muhimman ayyukan su. A matsayin su na masu kare muhalli, ‘yan jarida su kan fuskanci barazana, tsangwama, da tashin hankali saboda jajircewar su wajen fallasa laifukan muhalli da kare duniyar mu.”

Dangane da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, ministan ya ce dole ne mu sake jaddada aniyar mu ta kare haƙƙin ‘yan jarida da tabbatar da tsaron su.

“A matsayi na na Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, ina so in ƙara jaddada aniyar mu ta kare ‘yancin aikin jarida, inganta ra’ayoyi mabambanta, da kare haƙƙin ‘yan jarida.

“Mu ƙara zage damtse wajen gina makoma inda aikin jarida zai bunƙasa, a tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida, da kuma kare duniyar mu har zuwa al’ummomi masu zuwa.

“Yayin da mu ke gudanar da ayyukan mu, dole ne mu kuma tuna cewa Nijeriya, muhallin mu, ita ce abin da ya kamata mu fara karewa daga labaran ƙarya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MuhalliTabarbarewar tsaroTasirin Dimokiraɗiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Babin Diflomasiyyar: Kira Ga Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Next Post

Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

Related

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

1 hour ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

2 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

3 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

4 hours ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

6 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

8 hours ago
Next Post
Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.