• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cew a za ta ci gaba da bin umarnin da kowace kotu ta bayar a dukkan hukunce-hukuncen da su ka shafi zaɓe.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke jawabi wurin buɗe Taron Alƙalai na Ƙara wa Juna Ilmi Kan Zaɓen, wanda aka yi ranar Litinin a Cibiyar Inganta Harkokin Shari’a (NJC), a Abuja.

  • Mutum Miliyan 93.5 Ne Za Su Kada Kuri’a A Zaben 2023 – INEC

Ya ce: “An shirya irin wannan zama kafin zaɓen 2019, inda aka yi bitar rikice-rikicen ƙararrakin da za su taso bayan zaɓe. Kuma wancan taron da mu ka yi ya yi tasiri sosai a lokacin.

“Saboda an samu raguwar hukunce-hukuncen da kotuna ke bayarwa masu cin karo da juna. Kuma an samu raguwar yawan zaɓen da kotuna ke sokewa masu yawan gaske.”

Yakubu ya gode wa manyan alƙalai da Hukumar Kula da Shari’a ta Ƙasa dangane wannan taro mai muhimmanci, wanda ya ce babu shakka zai rage yawan ƙararrakin zaɓe a kotuna.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

INEC

Dangane da muhimmancin taron, Yakubu ya buga misali da irin matsalolin da ake samu a kotuna dalilin yanke hukunci masu karo da juna da kotuna ke yi.

Ya ce, “An samu wata kotu ta yi fatali da hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke, ta umarci INEC ta bayar da satifiket ɗin nasarar zaɓen fidda gwani ga ɗan takarar da Kotun Ƙoli ta soke zaɓen sa. To kun ga wannan cikas ne sosai ga hukumar zaɓe.

“Irin wannan kuma shi ke haifar da cinkoson shari’un zaɓe a kotu. Kuma an maida hannun agogo baya, tunda an sake shari’ar kenan wataƙila ma har sai an kai ga komawa Kotun Ƙoli.”

Haka kuma shugaban na INEC ya nuna damuwa dangane da yawaitar ƙararrakin da aka haɗa da aka da sunan INEC aka maka kotu har sama da 600, a zaɓen fidda gwanin ‘yan takarar jam’iyyu daban-daban.

Yakubu ya bayyana cikin damuwa cewa: “Ko kwanan nan wata jam’iyya ta zo a rana ɗaya ta kawo mana sunayen sabbin ‘yan takara 70 da ta ke so a cire sunayen na farkon da aka aiko mana, a maye gurbin su da sabbin da su ka kai mana.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar ‘Yansanda Ta Karyata Rahoton Kai Wa Ayarin Motocin Atiku Hari A Jihar Borno

Next Post

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

1 hour ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

13 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

18 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

19 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

20 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

21 hours ago
Next Post
ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.