• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da kasar Amurka ta dakatar da bayar da tallafi ga kasashen Afirka, akwai mutanen da suka yi fushi, da wasu da suka fara daukar matakai, amma ba wanda ya yi rokon afuwa.

A kwanakin nan, kasar Amurka ta sanar da kawo karshen kaso 83% na ayyukan da ake tafiyar da su karkashin tsarin hukumar USAID, lamarin da ya haifar da tsaiko ga yarjeniyoyin hadin gwiwa 5200. Dangane da matakai masu alaka da batun, dan jarida a fannin kimiyya da fasaha Abdullahi Tsanni, ya rubuta a cikin wata mukalar da aka wallafa cikin mujallar Science da cewa, “Daukacin kasashen nahiyar Afirka sun yi fushi matuka”, saboda “an soke kudin tallafawa aikin hana yaduwar cututtuka, da yawansa ya kai biliyoyin daloli, da dakatar da gwaje-gwajen fasahohin jinya ba zato ba tsammani, lamarin da ya sanya mutane fiye da dubu dari 1 fuskantar yiwuwar rasa rayuka.”

  • Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
  • Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 6 A Nasarawa

Sai dai bayan nuna takaici, ‘yan Afirka ba su daga tutar amana ko rokon afuwa ba. Maimakon haka, sun fara bincike a kai. Misali, Salim Karim, shugaban cibiyar nazarin cutar kanjamau ta kasar Afirka ta Kudu, ya ce janyewar tallafin Amurka wani gargadi ne ga kasashen Afirka, wanda ya nuna cewa “Kar a dogara da tallafin da sauran kasashen suke bayarwa wajen biyan bukatar kai, dole ne a yi kokarin dogaro da kai.”

A sa’i daya kuma, gwamnatocin kasashen Afirka sun fara daukar matakai. Inda a Najeriya, majalisar dattawa ta zartas da ware karin dalar Amurka miliyan dari 2 don tallafi a bangaren aikin jinya. Kana a kasashen Botswana, da Kamaru, da Kenya, hukumomi masu kula da aikin jinya sun yi alkawarin samar da kudin da ake bukata wajen kula da masu kamuwa da cutar kanjamau, yayin da gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta yi niyyar samar da kaso 83% na kudin da ake bukata a wannan bangare. Ko da yake akwai wuyar cike dukkan gibin da ke akwai ta fuskar kudin tafiyar da aikin jinya, amma dukkan kasashen Afirka sun nuna niyyar dogaro da kai. Hakan ya dace da maganar da shahararriyar masaniyar ilimin hana yaduwar cututtuka ta kasar Zimbabwe, Francisca Mutapi ta fada, wato “Kasashen yamma ba za su samar da dabarar daidaita matsalar aikin jinya a Afirka daga tushenta ba.”

Ma iya cewa karfin zuciya da kasashen Afirka suka nuna a wannan karo ya burge ni sosai, sai dai bai ba ni mamaki ba. Saboda na dade ina ganin alamar “farkar nahiyar Afirka”, da yadda kasashen Afirka suke daukar matakai bisa muradun kansu. Misali, bayan barkewar yaki tsakanin Ukraine da Rasha, kasashen Afirka sun ki daukar wani bangare tsakaninsu, ko da yake suna fuskantar matsin lamba daga kasashen yamma. Kana a fannin tattalin arziki, kasashen Afirka na kokarin gina wani babban yankin ciniki mai ‘yanci da ya shafi daukacin nahiyar Afirka. Yayin da a fannin tsaro, sun sa sojojin Faransa, da na Amurka janye jiki daga kasashen dake yammacin Afirka daya bayan daya.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka. Sai dai shugaban bai san sauye-sauyen da kasashen Afirka suka samu ba, wadanda tun tuni suka daina dogaro da kasashen yammacin duniya.

A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa

Next Post

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

11 hours ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

13 hours ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

3 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

3 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

4 days ago
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.