ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

Bayan da kasar Amurka ta dakatar da bayar da tallafi ga kasashen Afirka, akwai mutanen da suka yi fushi, da wasu da suka fara daukar matakai, amma ba wanda ya yi rokon afuwa.

A kwanakin nan, kasar Amurka ta sanar da kawo karshen kaso 83% na ayyukan da ake tafiyar da su karkashin tsarin hukumar USAID, lamarin da ya haifar da tsaiko ga yarjeniyoyin hadin gwiwa 5200. Dangane da matakai masu alaka da batun, dan jarida a fannin kimiyya da fasaha Abdullahi Tsanni, ya rubuta a cikin wata mukalar da aka wallafa cikin mujallar Science da cewa, “Daukacin kasashen nahiyar Afirka sun yi fushi matuka”, saboda “an soke kudin tallafawa aikin hana yaduwar cututtuka, da yawansa ya kai biliyoyin daloli, da dakatar da gwaje-gwajen fasahohin jinya ba zato ba tsammani, lamarin da ya sanya mutane fiye da dubu dari 1 fuskantar yiwuwar rasa rayuka.”

  • Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
  • Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 6 A Nasarawa

Sai dai bayan nuna takaici, ‘yan Afirka ba su daga tutar amana ko rokon afuwa ba. Maimakon haka, sun fara bincike a kai. Misali, Salim Karim, shugaban cibiyar nazarin cutar kanjamau ta kasar Afirka ta Kudu, ya ce janyewar tallafin Amurka wani gargadi ne ga kasashen Afirka, wanda ya nuna cewa “Kar a dogara da tallafin da sauran kasashen suke bayarwa wajen biyan bukatar kai, dole ne a yi kokarin dogaro da kai.”

ADVERTISEMENT

A sa’i daya kuma, gwamnatocin kasashen Afirka sun fara daukar matakai. Inda a Najeriya, majalisar dattawa ta zartas da ware karin dalar Amurka miliyan dari 2 don tallafi a bangaren aikin jinya. Kana a kasashen Botswana, da Kamaru, da Kenya, hukumomi masu kula da aikin jinya sun yi alkawarin samar da kudin da ake bukata wajen kula da masu kamuwa da cutar kanjamau, yayin da gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta yi niyyar samar da kaso 83% na kudin da ake bukata a wannan bangare. Ko da yake akwai wuyar cike dukkan gibin da ke akwai ta fuskar kudin tafiyar da aikin jinya, amma dukkan kasashen Afirka sun nuna niyyar dogaro da kai. Hakan ya dace da maganar da shahararriyar masaniyar ilimin hana yaduwar cututtuka ta kasar Zimbabwe, Francisca Mutapi ta fada, wato “Kasashen yamma ba za su samar da dabarar daidaita matsalar aikin jinya a Afirka daga tushenta ba.”

Ma iya cewa karfin zuciya da kasashen Afirka suka nuna a wannan karo ya burge ni sosai, sai dai bai ba ni mamaki ba. Saboda na dade ina ganin alamar “farkar nahiyar Afirka”, da yadda kasashen Afirka suke daukar matakai bisa muradun kansu. Misali, bayan barkewar yaki tsakanin Ukraine da Rasha, kasashen Afirka sun ki daukar wani bangare tsakaninsu, ko da yake suna fuskantar matsin lamba daga kasashen yamma. Kana a fannin tattalin arziki, kasashen Afirka na kokarin gina wani babban yankin ciniki mai ‘yanci da ya shafi daukacin nahiyar Afirka. Yayin da a fannin tsaro, sun sa sojojin Faransa, da na Amurka janye jiki daga kasashen dake yammacin Afirka daya bayan daya.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka. Sai dai shugaban bai san sauye-sauyen da kasashen Afirka suka samu ba, wadanda tun tuni suka daina dogaro da kasashen yammacin duniya.

A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 
Ra'ayi Riga

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.