ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

Bayan da kasar Amurka ta dakatar da bayar da tallafi ga kasashen Afirka, akwai mutanen da suka yi fushi, da wasu da suka fara daukar matakai, amma ba wanda ya yi rokon afuwa.

A kwanakin nan, kasar Amurka ta sanar da kawo karshen kaso 83% na ayyukan da ake tafiyar da su karkashin tsarin hukumar USAID, lamarin da ya haifar da tsaiko ga yarjeniyoyin hadin gwiwa 5200. Dangane da matakai masu alaka da batun, dan jarida a fannin kimiyya da fasaha Abdullahi Tsanni, ya rubuta a cikin wata mukalar da aka wallafa cikin mujallar Science da cewa, “Daukacin kasashen nahiyar Afirka sun yi fushi matuka”, saboda “an soke kudin tallafawa aikin hana yaduwar cututtuka, da yawansa ya kai biliyoyin daloli, da dakatar da gwaje-gwajen fasahohin jinya ba zato ba tsammani, lamarin da ya sanya mutane fiye da dubu dari 1 fuskantar yiwuwar rasa rayuka.”

  • Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
  • Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 6 A Nasarawa

Sai dai bayan nuna takaici, ‘yan Afirka ba su daga tutar amana ko rokon afuwa ba. Maimakon haka, sun fara bincike a kai. Misali, Salim Karim, shugaban cibiyar nazarin cutar kanjamau ta kasar Afirka ta Kudu, ya ce janyewar tallafin Amurka wani gargadi ne ga kasashen Afirka, wanda ya nuna cewa “Kar a dogara da tallafin da sauran kasashen suke bayarwa wajen biyan bukatar kai, dole ne a yi kokarin dogaro da kai.”

ADVERTISEMENT

A sa’i daya kuma, gwamnatocin kasashen Afirka sun fara daukar matakai. Inda a Najeriya, majalisar dattawa ta zartas da ware karin dalar Amurka miliyan dari 2 don tallafi a bangaren aikin jinya. Kana a kasashen Botswana, da Kamaru, da Kenya, hukumomi masu kula da aikin jinya sun yi alkawarin samar da kudin da ake bukata wajen kula da masu kamuwa da cutar kanjamau, yayin da gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta yi niyyar samar da kaso 83% na kudin da ake bukata a wannan bangare. Ko da yake akwai wuyar cike dukkan gibin da ke akwai ta fuskar kudin tafiyar da aikin jinya, amma dukkan kasashen Afirka sun nuna niyyar dogaro da kai. Hakan ya dace da maganar da shahararriyar masaniyar ilimin hana yaduwar cututtuka ta kasar Zimbabwe, Francisca Mutapi ta fada, wato “Kasashen yamma ba za su samar da dabarar daidaita matsalar aikin jinya a Afirka daga tushenta ba.”

Ma iya cewa karfin zuciya da kasashen Afirka suka nuna a wannan karo ya burge ni sosai, sai dai bai ba ni mamaki ba. Saboda na dade ina ganin alamar “farkar nahiyar Afirka”, da yadda kasashen Afirka suke daukar matakai bisa muradun kansu. Misali, bayan barkewar yaki tsakanin Ukraine da Rasha, kasashen Afirka sun ki daukar wani bangare tsakaninsu, ko da yake suna fuskantar matsin lamba daga kasashen yamma. Kana a fannin tattalin arziki, kasashen Afirka na kokarin gina wani babban yankin ciniki mai ‘yanci da ya shafi daukacin nahiyar Afirka. Yayin da a fannin tsaro, sun sa sojojin Faransa, da na Amurka janye jiki daga kasashen dake yammacin Afirka daya bayan daya.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Hakika yadda kasar Amurka ta dakatar da tallafi a wannan karo ya nuna ra’ayin shugaba Donald Trump dangane da kasashen Afirka. Wanda za a iya fahimta bisa ganin yadda ya bayyana kasar Lesotho a matsayin “kasar da ba a san ta ba”, wacce ba ta cancanci tallafin da ake ba ta ba, a kwanakin baya, yayin da yake magana da ‘yan majalisun kasar Amurka. Sai dai shugaban bai san sauye-sauyen da kasashen Afirka suka samu ba, wadanda tun tuni suka daina dogaro da kasashen yammacin duniya.

A daura da haka, ana iya ganin fahimtar matsayin kasashen Afirka mai dacewa, a cikin maganar da ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada a kwanan baya, yayin da yake amsa tambayar da wakiliyar kafar yada labaru ta Najeriya NAN ta gabatar masa. Inda ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin wuri mai muhimmanci a karni na 21, wanda samun kwanciyar hankali da ci gaban tattalin arzikinsa ya shafi makomar bai daya ta daukacin dan Adam. Sa’an nan, bayan da ya yi bayani kan kokarin da kasar Sin ta yi wajen haifar da takamaiman ci gaba a kasashen Afirka, jami’in na Sin ya ce, “Nahiyar Afirka na cikin wani sabon mataki na farkawa. Kamata ya yi a mara musu baya, don su iya dogaro da kai wajen tafiya a kan sabuwar turbarsu ta raya kasa.” (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan’Adam 18 Daga Cibiyar Harba Kumbo Ta Kasuwanci Ta Hainan

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.