• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 

by Khalid Idris Doya, Sulaiman and CGTN Hausa
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da jawabi ga al’umman kasa cikin bukukuwan ranar samun ‘yancin kai karo na 64, inda ya ce, sabbin manufofi da tsare-tsarensa sun fara ba da sakamakon da ake nema. 

 

Ya kuma sanar da aniyar gwamnatinsa na shigo da matasa a dama da su a cikin gwamnatinsa da ba su damarmaki ta hanyar gudanar da babban taron matasa na kasa na kwanaki 30.

 

Ga muhimman abubuwa 10 da jawabin Tinubu ya kunsa kamar haka:

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Amincewa Da Matsalolin Da Suke Jibge: Tinubu ya ce, yana sane da irin yadda ‘yan Nijeriya da dama ke shan wahalar tsadar rayuwa, tsadar kayan abinci da matsalar rashin ayyukan yi. Ya ba da tabbacin shawo kansu.

 

Jajircewa: Tinubu ya yi tsokaci kan ci gaban da Nijeriya ta samu tun bayan samun ‘yancin kai, ya lura kan cewa kasar ta samu tsayuwa da kanta duk da rikice-rikice irinsu yakin basasa, da dai sauransu.

 

Yunkurin Samar Da Tsaro: Ya bayyana muhimman nasarorin da ake samu wajen yaki da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, da sauran nau’ikan ayyukan ta’addanci. Ya samar da kashe sama da kwamandoji 30 na Boko Haram da sauran kungiyoyin masu dauke da bindigogi.

 

Farfado Da Tattalin Arziki: Tinubu ya jaddada wajibcin yin garambawul ga tsare-tsaren tattalin arzikin domin shawo kan matsalolin da suke jibge a sha’anin kudi. Ya ce wannan yunkurin ya kai ga janyo dala biliyan 30 na zuba hannun jarin kasashen waje da kuma inganta hada-hadar kudade.

 

Yunkurin Rage Matsin Rayuwa: Tinubu ya amince da irin wahalar da jama’a ke sha da matsin rayuwa, musamman kan tsadar farashin kayayyakin abinci, har ma ya ce, “Babban abun da ya fi damun mutanenmu a yau shi ne tsadar rayuwa, musamman kan kayayyakin abinci. Wannan lamarin ya shafi mutane da dama a fadin duniya, inda farashin da tsadar rayuwa ke ci gaba da faruwa a fadin duniya. “Muna sa ran ganin an samu karin amfanin da ake fitarwa da kuma raguwar tsadar kayan abinci.

 

Samar Da Ayyuka Ga Matasa: Shugaban ya sanar da shirin gudanar da babban taron matasa na kasa da kuma wasu shirye-shiryen da aka ware su kai tsaye ga matasa ciki kuwa har da shirin 3MTT na baje fasaha da kuma asusun rancen ilimi na Nijeriya. “Wannan babban taron zai taimaki matasanmu su samu shiga a dama da su a cikin gudanar da mulki.”

 

‘Yancin Cin Kashin Kan Kananan Hukumomi A Bangaren Kudade: Tinubu ya jaddada aniyarsa na aiwatar da hukuncin umarnin kotun koli na bai wa kananan hukumomi kason kudadensu kai tsaye.

 

Shirye-shirye Kan Makamashi Da Sufuri: Ya sanar da shirinsa na fadada rungumar motocin da ke amfani da iskar gas. Ya ce, “Yunkurinmu na kyautata makamashi na tafi kan turba. Muna fadada shirinmu na amfani da motoci masu amfani da iskar gas a bangaren sufuri. Gwamnatin tarayya a shirye take ta mara wa jihohi 36 ciki har da Babban Birnin Tarayya baya da su mallaki motocin domin saukaka wa jama’a sufuri.”

 

Rage Radadin Annoba Da Matakan Kariya: Shugaban kasa ya kuma yi magana kan yunkurin gwamanti na tunkarar ibtila. Ya ce, “Gwamnatinmu na tunkarar ibtila da aka samu baya-bayan nan, musamman ma na ambaliyar ruwa a wasu sassan kasa. Bayan ziyarar da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya kai Maiduguri, Ni ma da kaina na je na ziyarci garin domin tabbatar wa jama’anmu cewa wannan gwamnatin tarayyar a kowani lokaci tana tare da mutanenta a kowani lokaci. A taron karshe na majalisar koli ta kasa, mun amince da samar da asusun kula da ibtila’i da samar da yanayin da masu kamfanoni da daidaiku za su taimaka mana wajen tunkarar matsaloli cikin gaggawa.

 

Kyakkyawar Fata Ga Ci Gaba: Ya karkare jawabinsa da karfafan ‘yan Nijeriya da cewa, ka da su yanke kauna, su ci gaba da jajircewa da yin aikin hadin gwiwa domin ci gaba da kuma rayuwar gobe. Ya kuma nanata aniyar gwamnatinsa na kara shigo da kowani bangare da samar da ci gaba mai dorewa da kuma hadin kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yancin KaiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Next Post

Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

Related

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

4 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

4 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

8 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

19 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

20 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

22 hours ago
Next Post
Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.