ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 

by Khalid Idris Doya, Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da jawabi ga al’umman kasa cikin bukukuwan ranar samun ‘yancin kai karo na 64, inda ya ce, sabbin manufofi da tsare-tsarensa sun fara ba da sakamakon da ake nema. 

 

Ya kuma sanar da aniyar gwamnatinsa na shigo da matasa a dama da su a cikin gwamnatinsa da ba su damarmaki ta hanyar gudanar da babban taron matasa na kasa na kwanaki 30.

ADVERTISEMENT

 

Ga muhimman abubuwa 10 da jawabin Tinubu ya kunsa kamar haka:

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Amincewa Da Matsalolin Da Suke Jibge: Tinubu ya ce, yana sane da irin yadda ‘yan Nijeriya da dama ke shan wahalar tsadar rayuwa, tsadar kayan abinci da matsalar rashin ayyukan yi. Ya ba da tabbacin shawo kansu.

 

Jajircewa: Tinubu ya yi tsokaci kan ci gaban da Nijeriya ta samu tun bayan samun ‘yancin kai, ya lura kan cewa kasar ta samu tsayuwa da kanta duk da rikice-rikice irinsu yakin basasa, da dai sauransu.

 

Yunkurin Samar Da Tsaro: Ya bayyana muhimman nasarorin da ake samu wajen yaki da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, da sauran nau’ikan ayyukan ta’addanci. Ya samar da kashe sama da kwamandoji 30 na Boko Haram da sauran kungiyoyin masu dauke da bindigogi.

 

Farfado Da Tattalin Arziki: Tinubu ya jaddada wajibcin yin garambawul ga tsare-tsaren tattalin arzikin domin shawo kan matsalolin da suke jibge a sha’anin kudi. Ya ce wannan yunkurin ya kai ga janyo dala biliyan 30 na zuba hannun jarin kasashen waje da kuma inganta hada-hadar kudade.

 

Yunkurin Rage Matsin Rayuwa: Tinubu ya amince da irin wahalar da jama’a ke sha da matsin rayuwa, musamman kan tsadar farashin kayayyakin abinci, har ma ya ce, “Babban abun da ya fi damun mutanenmu a yau shi ne tsadar rayuwa, musamman kan kayayyakin abinci. Wannan lamarin ya shafi mutane da dama a fadin duniya, inda farashin da tsadar rayuwa ke ci gaba da faruwa a fadin duniya. “Muna sa ran ganin an samu karin amfanin da ake fitarwa da kuma raguwar tsadar kayan abinci.

 

Samar Da Ayyuka Ga Matasa: Shugaban ya sanar da shirin gudanar da babban taron matasa na kasa da kuma wasu shirye-shiryen da aka ware su kai tsaye ga matasa ciki kuwa har da shirin 3MTT na baje fasaha da kuma asusun rancen ilimi na Nijeriya. “Wannan babban taron zai taimaki matasanmu su samu shiga a dama da su a cikin gudanar da mulki.”

 

‘Yancin Cin Kashin Kan Kananan Hukumomi A Bangaren Kudade: Tinubu ya jaddada aniyarsa na aiwatar da hukuncin umarnin kotun koli na bai wa kananan hukumomi kason kudadensu kai tsaye.

 

Shirye-shirye Kan Makamashi Da Sufuri: Ya sanar da shirinsa na fadada rungumar motocin da ke amfani da iskar gas. Ya ce, “Yunkurinmu na kyautata makamashi na tafi kan turba. Muna fadada shirinmu na amfani da motoci masu amfani da iskar gas a bangaren sufuri. Gwamnatin tarayya a shirye take ta mara wa jihohi 36 ciki har da Babban Birnin Tarayya baya da su mallaki motocin domin saukaka wa jama’a sufuri.”

 

Rage Radadin Annoba Da Matakan Kariya: Shugaban kasa ya kuma yi magana kan yunkurin gwamanti na tunkarar ibtila. Ya ce, “Gwamnatinmu na tunkarar ibtila da aka samu baya-bayan nan, musamman ma na ambaliyar ruwa a wasu sassan kasa. Bayan ziyarar da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya kai Maiduguri, Ni ma da kaina na je na ziyarci garin domin tabbatar wa jama’anmu cewa wannan gwamnatin tarayyar a kowani lokaci tana tare da mutanenta a kowani lokaci. A taron karshe na majalisar koli ta kasa, mun amince da samar da asusun kula da ibtila’i da samar da yanayin da masu kamfanoni da daidaiku za su taimaka mana wajen tunkarar matsaloli cikin gaggawa.

 

Kyakkyawar Fata Ga Ci Gaba: Ya karkare jawabinsa da karfafan ‘yan Nijeriya da cewa, ka da su yanke kauna, su ci gaba da jajircewa da yin aikin hadin gwiwa domin ci gaba da kuma rayuwar gobe. Ya kuma nanata aniyar gwamnatinsa na kara shigo da kowani bangare da samar da ci gaba mai dorewa da kuma hadin kai.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
  • Sulaiman
    Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Tinubu
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Tinubu
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Tinubu

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Tinubu

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Tinubu

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.