• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

byMuhammad
3 months ago
Buhari

An haifi Muhammadu Buhari a ranar 17, ga Disamba, 1942, a garin Daura na Jihar Katsina, Nijeriya. Shi ne ɗa na 23 a cikin yaran Malam Harɗo Adamu, wani shugaba Fulani da ya fito daga garin Dumurkul da ke ƙaramar hukumar Mai’Adua ta jihar Katsina, da mahaifiyarsa Zulaihat. 

Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari shi ne mutum na shida da aka zaɓa ta hanyar dimokuraɗiyya a Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya rasu yana da shekaru 82 (2025 – 1942) a yammacin a ranar Lahadi a wani asibiti da ke birnin Landan bayan ya sha fama da doguwar rashin lafiya.

  • Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan
  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan

Ga wasu manyan abubuwa 10 da kowa zai so ya sani game da rayuwar Marigayi Buhari:

1. Hawa Shugabanci Karo Biyu – Soja Da Siyasa
Buhari ya shugabanci Nijeriya a matsayin shugaban mulkin soja daga 1983 zuwa 1985, sannan kuma aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a 2015 zuwa 2023.

2. Ƙwararren Soja, Ɗan Yaƙin Basasa
Ya shiga soja a 1962, ya samu horo a Burtaniya, kuma ya yi yaki a lokacin yaƙin basasa, inda ya jagoranci bataliya da manyan hare-hare a yankin gabas.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

3. Ƙaddamar Da Yaƙi Da Rashin Ɗa’a (WAI)
A mulkinsa na soja, Buhari ya ƙaddamar da shahararren shirin yaƙi da rashin ɗa’a, don ya gyara halayen jama’a da ƙarfafa kyawawan ɗabi’u da kishin ƙasa.

4. Mulki Tsauri A Shekarun 1980
Mulkinsa na soja ya ƙunshi dokoki masu tsauri da daure ’yan jarida da sallamar ma’aikata daj yanke hukuncin kisa ga masu safarar miyagun ƙwayoyi.

5. Shugabantar Kula Da Asusun PTF
A ƙarƙashin mulkin Janar Abacha, Buhari ya shugabanci PTF, inda aka yabawa ayyukansa na1 gaskiya da gina ababen more rayuwa.

6. Ya Yi Takara Huɗu, Ya Ci Zaɓe A Karo Na Ƙarshe
Buhari ya tsaya takara a 2003 da 2007 da 2011, amma sai a shekarar 2015 ya lashe zaɓe a matsayin shugaban ƙasa kuma ɗan jam’iyyar APC, inda ya kayar da Shugaba Goodluck Jonathan.

7. Ya Mayar Da Hankali Kan Yaƙi Da Rashawa Da Samar Da Tsaro
A mulkinsa na farar hula, ya mayar da hankali kan yaƙi da rashawa da yaƙi da Boko Haram da samar da shirye-shiryen tallafawa matasa kamar shirin N-Power.

8. Doguwar Jinya Ta Yi Tasiri A Mulkinsa
Ya sha barin ƙasa don neman lafiya, ciki har da watanni huɗu a 2017, lamarin da ya jawo damuwa da firgici kan yanayin lafiyarsa da tafiyar da mulki.

9. Ƙalubalen Zanga-Zangar #EndSARS
A 2020, gwamnatinsa ta fuskanci babbar zanga-zangar matasa kan cin zarafin ’yansanda (#EndSARS), wadda ta zama jigo a tarihin mulkinsa.

10. Miƙa Mulki Cikin Lumana Da Komawa Daura
A ranar 29 ga Mayu, 2023, ya miƙa mulki ga Shugaba Tinubu, sannan ya koma mahaifarsa garin Daura na jihar Katsina, bayan ya kammala aikin gwamnati na aƙaalla shekaru 50.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Next Post
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version