• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 7 Game Da Raya Huldar Sin Da Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Amurka

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a birnin Lima, hedkwatar kasar Peru, inda suka yi musanyar ra’ayi mai zurfi cikin sahihanci, kan huldar kasashen biyu da harkokin kasa da kasa.

 

Yayin ganawar, bangaren Sin ya bayyana za a rungumi sahihanci da yin kokari wajen raya huldar kasashen biyu, tare da shugaba Biden, da kuma mai karbar ragamar mukaminsa, a daidai wannan lokaci da ake daf da mika mulkin Amurka ga sabuwar gwamnati.

  • Xi Jinping: Alakar Sin Da Brazil Ta Kai Wani Muhimmin Mataki A Tarihi
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

A cikin shekaru 45 da suka gabata tun kafuwar huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu, duk da cewa ana fuskantar sauye-sauyen yanayin duniya, Sin na nacewa ra’ayin cudanyar abota a maimakon kulla gaba da juna, da kuma cimma moriyar juna a maimakon haifar wa juna illa, kana da amincewa da banbancin ra’ayi, tare da kokarin cimma matsaya daya a maimakon yin takara ba bisa doka ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Shaidu na hakika sun bayyana cewa, Amurka ta matsa lamba, tana kokarin dakile bunkasuwar Sin bisa matsayinta na wai “mafi karfi a duniya”, ko da yake hakan ba zai cimma nasara ba ko kadan, a maimakon haka matakin ya illata moriyarta, kuma ya kara rura wutar fito-na-fito a duniya.

 

Sin da Amurka na da nauyi mai muhimmanci a bangaren kiyaye zaman lafiyar duniya, da kara azama ga bunkasuwarsu tare, don haka dole ne su yi kokarin ba da tabbaci, da amfani mai yakini ga duniya wadda ke fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice.

 

Sin na fatan bangarorin biyu za su nace ga ka’idar mutunta juna, da zama tare cikin lumana, da haifar da moriyar juna, da kuma bin jagorancin da shugaba Xi Jinping ya gabatar, wato muhimman abubuwa 7 na raya huldar kasashen biyu, ta yadda za a daidaita huldarsu cikin lumana, don fitar da wata hanya da ta dace ta raya huldar sassan biyu, ta yadda hakan zai amfani kasashen biyu har ma da duniya baki daya. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Ce Babu Wani Rikici Na Nuna Son Kai Tsakanin Sin Da Australia

Xi Jinping Ya Ce Babu Wani Rikici Na Nuna Son Kai Tsakanin Sin Da Australia

LABARAI MASU NASABA

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.