• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Batutuwan Da Aka Tattaunawa Tsakanin Shugaba Tinubu Da ‘Yan Jarida

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba kasa Bola Tinubu ya tattauna da ‘yan jarida na kusan awa daya a ranar Litinin a gidansa da ke Legas. Wannan shi ne tattaunawarsa ta farko a kafafen yada labarai tun bayan da ya hau kan karagar mulki kimanin watanni 18 da suka gabata.

Muhimman batutuwan da aka tattauna sun hada da cire tallafin man fetur, kudirin sake lissafin haraji, sake fasalin tattalin arziki, fadin girman gwamnatinsa da kuma cin hanci da rashawa.

  • Sojoji Sun Daƙile Harin Jirgi Mara Matuƙi A Yobe
  • Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

A yayin da yake amsa tambayoyin manema labari, Shugaba Tinubu ya yi watsi da yadda ake sukar gwamnatinsa kan fadin girmanta, sannan kuma ya ce ba zai rage yawan majalisar ministocinsa ba.

 

“Ban shirya rage girman majalisar ministocina ba. Na ga muhimmancin hada su wuri guda. Ba na bai wa wani aikin da ba zai iya yi ba,” in ji shugaba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

Shugaba Tinubu ya kuma yi magana kan matsalar tsadar rayuwa a kasar nan. Ga miliyoyin ’yan Nijeriya, manufofin gwamnati, kamar cire tallafin man fetur da kuma kaiya darajar naira, sun jawo matsin tattalin arziki a Nijeriya.

Ya jaddada cewa ya yi abin da ya dace ta hanyar sanar da cire tallafin man fetur a bikin rantsar da shi a bara. “Ba na nadamar cire tallafin man fetur,” in ji shi.

 

Lakacin da aka tambaye shi ko gwamnatinsa za ta duba yuwuwar yadda za a shawo kan farashin kayayyaki don duba tsadar kayayyaki da ayyuka, shugaban na Nijeriya ya ce bai yarda da yadda gwamnati za ta kula da farashin kayayyaki ba. “Muna ci gaba da samar da harkokin kasuwa, muna aiki tukuru don samar kasuwanci mai dorewa”.

Ya kuma bayyana gamsuwarsa da yanayin tsaron kasar nan, sannan ya yaba wa hafsoshin tsaron bisa kwazon da suka yi wajen samar da tsaro a kasar nan. “Ina alfahari da abin da suke yi a yau,” in ji shugaban.

An gurfanar da tsofaffin manyan jami’an sojoji da suka hada da na sojan kasa da na sama, da kuma tsohon mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, wanda ya yi aiki a gwamnatocin baya, bisa zargin satar dukiyar al’umma a lokacin da suke kan karagar mulki.

Amma duk da haka, Shugaba Tinubu ya ce ba zai binciki duk wani shugaban tsaro ba. Lokacin da aka tambaye shi ko yana da shirin yin hakan. “Ba za ku raina cibiyar tsaro ba saboda barazanar bincike,” in ji shi.

Hakazalika, shugaban Nijeriya ya kuma yi magana kan kudirin sake fasalin haraji da ke gaban majalisar dokokin kasar. Ya ce gyaran harajin yana bukatar tattaunawa da rangwame, kuma kafarsa a bude take kan hakan.

Kudirin dokar dai ya fuskanci adawa mai zafi daga sassan arewacin kasar nan, musamman daga wasu gwamnonin da suka bayyana shi a matsayin kudirin da zai kashe arewa.

Sai dai kuma Tinubu ya ce babu gudu, babu ja da baya a kan kudirin sake fasalin haraji a Nijeriya.

Mista Tinubu ya kuma bayar da hujjar karbar bashin kudade daga cibiyoyin hada-hadar kudi na duniya domin cike gibin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2025. Ya ce samun lamuni ba laifi ba ne, domin ana yin amfani da irin wadannan lamuni ne wajen bunkasa ababen more rayuwa a kasa.

Yayin da shugaban ya yi imanin ba za a iya kawar da cin hanci da rashawa ba, ya ce za a iya rage shi zuwa mafi kankanta tare da aiwatar da wasu hanyoyin za su hana faruwar hakan. Tinubu ya bayyana shirin rancen dalibai da tsarin biyan mafi karin karancin albashi da kuma cire tallafin man fetur a matsayin kokarin gwamnatinsa na hana cin hanci da rashawa.

Shugaban ya kuma zargi wadanda suka shirya rabon tallafi da hannu dumu-dumu wajen ibtila’in turmutsisin da ya faru a Oyo, Anambra, da Abuja, Babban Birnin Nijeriya. “Ina ganin wannan a matsayin babban kuskure daga bangaren masu shirya bayar da tallafin,” in ji shugaban na Nijeriya. Sama da mutane 60 da suka hada da kananan yara ne suka mutu a wanann lamari da ya faru a jihohin uku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin NNPCL Ya Rage Farashin Litar Mai Zuwa Naira 965 A Abuja

Next Post

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Related

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

2 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

4 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

4 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

16 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

17 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta'adda A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.