• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Batutuwan Da Aka Tattaunawa Tsakanin Shugaba Tinubu Da ‘Yan Jarida

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
tinubu

Shugaba kasa Bola Tinubu ya tattauna da ‘yan jarida na kusan awa daya a ranar Litinin a gidansa da ke Legas. Wannan shi ne tattaunawarsa ta farko a kafafen yada labarai tun bayan da ya hau kan karagar mulki kimanin watanni 18 da suka gabata.

Muhimman batutuwan da aka tattauna sun hada da cire tallafin man fetur, kudirin sake lissafin haraji, sake fasalin tattalin arziki, fadin girman gwamnatinsa da kuma cin hanci da rashawa.

  • Sojoji Sun Daƙile Harin Jirgi Mara Matuƙi A Yobe
  • Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

A yayin da yake amsa tambayoyin manema labari, Shugaba Tinubu ya yi watsi da yadda ake sukar gwamnatinsa kan fadin girmanta, sannan kuma ya ce ba zai rage yawan majalisar ministocinsa ba.

 

“Ban shirya rage girman majalisar ministocina ba. Na ga muhimmancin hada su wuri guda. Ba na bai wa wani aikin da ba zai iya yi ba,” in ji shugaba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Shugaba Tinubu ya kuma yi magana kan matsalar tsadar rayuwa a kasar nan. Ga miliyoyin ’yan Nijeriya, manufofin gwamnati, kamar cire tallafin man fetur da kuma kaiya darajar naira, sun jawo matsin tattalin arziki a Nijeriya.

Ya jaddada cewa ya yi abin da ya dace ta hanyar sanar da cire tallafin man fetur a bikin rantsar da shi a bara. “Ba na nadamar cire tallafin man fetur,” in ji shi.

 

Lakacin da aka tambaye shi ko gwamnatinsa za ta duba yuwuwar yadda za a shawo kan farashin kayayyaki don duba tsadar kayayyaki da ayyuka, shugaban na Nijeriya ya ce bai yarda da yadda gwamnati za ta kula da farashin kayayyaki ba. “Muna ci gaba da samar da harkokin kasuwa, muna aiki tukuru don samar kasuwanci mai dorewa”.

Ya kuma bayyana gamsuwarsa da yanayin tsaron kasar nan, sannan ya yaba wa hafsoshin tsaron bisa kwazon da suka yi wajen samar da tsaro a kasar nan. “Ina alfahari da abin da suke yi a yau,” in ji shugaban.

An gurfanar da tsofaffin manyan jami’an sojoji da suka hada da na sojan kasa da na sama, da kuma tsohon mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, wanda ya yi aiki a gwamnatocin baya, bisa zargin satar dukiyar al’umma a lokacin da suke kan karagar mulki.

Amma duk da haka, Shugaba Tinubu ya ce ba zai binciki duk wani shugaban tsaro ba. Lokacin da aka tambaye shi ko yana da shirin yin hakan. “Ba za ku raina cibiyar tsaro ba saboda barazanar bincike,” in ji shi.

Hakazalika, shugaban Nijeriya ya kuma yi magana kan kudirin sake fasalin haraji da ke gaban majalisar dokokin kasar. Ya ce gyaran harajin yana bukatar tattaunawa da rangwame, kuma kafarsa a bude take kan hakan.

Kudirin dokar dai ya fuskanci adawa mai zafi daga sassan arewacin kasar nan, musamman daga wasu gwamnonin da suka bayyana shi a matsayin kudirin da zai kashe arewa.

Sai dai kuma Tinubu ya ce babu gudu, babu ja da baya a kan kudirin sake fasalin haraji a Nijeriya.

Mista Tinubu ya kuma bayar da hujjar karbar bashin kudade daga cibiyoyin hada-hadar kudi na duniya domin cike gibin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2025. Ya ce samun lamuni ba laifi ba ne, domin ana yin amfani da irin wadannan lamuni ne wajen bunkasa ababen more rayuwa a kasa.

Yayin da shugaban ya yi imanin ba za a iya kawar da cin hanci da rashawa ba, ya ce za a iya rage shi zuwa mafi kankanta tare da aiwatar da wasu hanyoyin za su hana faruwar hakan. Tinubu ya bayyana shirin rancen dalibai da tsarin biyan mafi karin karancin albashi da kuma cire tallafin man fetur a matsayin kokarin gwamnatinsa na hana cin hanci da rashawa.

Shugaban ya kuma zargi wadanda suka shirya rabon tallafi da hannu dumu-dumu wajen ibtila’in turmutsisin da ya faru a Oyo, Anambra, da Abuja, Babban Birnin Nijeriya. “Ina ganin wannan a matsayin babban kuskure daga bangaren masu shirya bayar da tallafin,” in ji shugaban na Nijeriya. Sama da mutane 60 da suka hada da kananan yara ne suka mutu a wanann lamari da ya faru a jihohin uku.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta'adda A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.