ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Batutuwan Da Aka Tattaunawa Tsakanin Shugaba Tinubu Da ‘Yan Jarida

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
tinubu

Shugaba kasa Bola Tinubu ya tattauna da ‘yan jarida na kusan awa daya a ranar Litinin a gidansa da ke Legas. Wannan shi ne tattaunawarsa ta farko a kafafen yada labarai tun bayan da ya hau kan karagar mulki kimanin watanni 18 da suka gabata.

Muhimman batutuwan da aka tattauna sun hada da cire tallafin man fetur, kudirin sake lissafin haraji, sake fasalin tattalin arziki, fadin girman gwamnatinsa da kuma cin hanci da rashawa.

  • Sojoji Sun Daƙile Harin Jirgi Mara Matuƙi A Yobe
  • Babu Sauran Burbushin ‘Yan Ta’addan Lakurawa A Arewa Maso Yamma – Ministan Tsaro

A yayin da yake amsa tambayoyin manema labari, Shugaba Tinubu ya yi watsi da yadda ake sukar gwamnatinsa kan fadin girmanta, sannan kuma ya ce ba zai rage yawan majalisar ministocinsa ba.

ADVERTISEMENT

 

“Ban shirya rage girman majalisar ministocina ba. Na ga muhimmancin hada su wuri guda. Ba na bai wa wani aikin da ba zai iya yi ba,” in ji shugaba.

LABARAI MASU NASABA

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Shugaba Tinubu ya kuma yi magana kan matsalar tsadar rayuwa a kasar nan. Ga miliyoyin ’yan Nijeriya, manufofin gwamnati, kamar cire tallafin man fetur da kuma kaiya darajar naira, sun jawo matsin tattalin arziki a Nijeriya.

Ya jaddada cewa ya yi abin da ya dace ta hanyar sanar da cire tallafin man fetur a bikin rantsar da shi a bara. “Ba na nadamar cire tallafin man fetur,” in ji shi.

 

Lakacin da aka tambaye shi ko gwamnatinsa za ta duba yuwuwar yadda za a shawo kan farashin kayayyaki don duba tsadar kayayyaki da ayyuka, shugaban na Nijeriya ya ce bai yarda da yadda gwamnati za ta kula da farashin kayayyaki ba. “Muna ci gaba da samar da harkokin kasuwa, muna aiki tukuru don samar kasuwanci mai dorewa”.

Ya kuma bayyana gamsuwarsa da yanayin tsaron kasar nan, sannan ya yaba wa hafsoshin tsaron bisa kwazon da suka yi wajen samar da tsaro a kasar nan. “Ina alfahari da abin da suke yi a yau,” in ji shugaban.

An gurfanar da tsofaffin manyan jami’an sojoji da suka hada da na sojan kasa da na sama, da kuma tsohon mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, wanda ya yi aiki a gwamnatocin baya, bisa zargin satar dukiyar al’umma a lokacin da suke kan karagar mulki.

Amma duk da haka, Shugaba Tinubu ya ce ba zai binciki duk wani shugaban tsaro ba. Lokacin da aka tambaye shi ko yana da shirin yin hakan. “Ba za ku raina cibiyar tsaro ba saboda barazanar bincike,” in ji shi.

Hakazalika, shugaban Nijeriya ya kuma yi magana kan kudirin sake fasalin haraji da ke gaban majalisar dokokin kasar. Ya ce gyaran harajin yana bukatar tattaunawa da rangwame, kuma kafarsa a bude take kan hakan.

Kudirin dokar dai ya fuskanci adawa mai zafi daga sassan arewacin kasar nan, musamman daga wasu gwamnonin da suka bayyana shi a matsayin kudirin da zai kashe arewa.

Sai dai kuma Tinubu ya ce babu gudu, babu ja da baya a kan kudirin sake fasalin haraji a Nijeriya.

Mista Tinubu ya kuma bayar da hujjar karbar bashin kudade daga cibiyoyin hada-hadar kudi na duniya domin cike gibin kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2025. Ya ce samun lamuni ba laifi ba ne, domin ana yin amfani da irin wadannan lamuni ne wajen bunkasa ababen more rayuwa a kasa.

Yayin da shugaban ya yi imanin ba za a iya kawar da cin hanci da rashawa ba, ya ce za a iya rage shi zuwa mafi kankanta tare da aiwatar da wasu hanyoyin za su hana faruwar hakan. Tinubu ya bayyana shirin rancen dalibai da tsarin biyan mafi karin karancin albashi da kuma cire tallafin man fetur a matsayin kokarin gwamnatinsa na hana cin hanci da rashawa.

Shugaban ya kuma zargi wadanda suka shirya rabon tallafi da hannu dumu-dumu wajen ibtila’in turmutsisin da ya faru a Oyo, Anambra, da Abuja, Babban Birnin Nijeriya. “Ina ganin wannan a matsayin babban kuskure daga bangaren masu shirya bayar da tallafin,” in ji shugaban na Nijeriya. Sama da mutane 60 da suka hada da kananan yara ne suka mutu a wanann lamari da ya faru a jihohin uku.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?
  • Sulaiman
    Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP
  • Sulaiman
    Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
  • Sulaiman
    Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
Labarai

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
Labarai

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta'adda A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.