• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

by Abubakar Abba
3 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shirin inganta noma na musamman (SAPZ), an kirkiro shi ne, domin habaka fannin aikin noma a wasu jihohin kasar nan da aka zabo.

 

An ware wa aikin biliyoyin Nairori, wanda zai samar da riba mai dimbin yawa ga fannin na aikin noma.

  • 2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed
  • Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

Aikin ya samu goyon bayan Bankin Bunkasa Aikin Noma a Afirka (AfDB), Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa da Kasa (IFAD), Bankin Raya Addinin Muslunci (ISDB).

 

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Kazalika, a cikin daukacin gwamnatin tarayya da kuma na jihohin kasar, an tsara yadda za su dakile kalubalen da fannin aikin noma da kuma yadda za a sama wa manoman kasar sauki, bunkasa rayuwar mazauna karkara da kuma habaka tattalin arzikin kasar.

 

Akasarin manufar aikin na SAPZ shi ne, domin inganta aikin noma a karkara, maimakon fitar da amfanin gona kamar irin su Rogo, Shinkafa, Tumatir da kuma Koko zuwa birane ko kuma kasar waje, za a tanadar da kayan aiki a yankunan da aka tsara za su amfana da shirin, domin manoman yankin su samu ribar da ta kamata.

 

Daya daga cikin manyan matsalolin da ake samu a Nijeriya ita ce, gibin da ake samu a bangaren aikin noma domin samun riba.

 

Amma a wadannan yankunan da za a gudanar da aikin, za a samar da masana’antun sarrafa amfanin gona, kayan adana amfanin gona, wutar lantarki mai dorewa, tituna da kuma cibiyoyin bayar da horo.

 

Nijeriya dai, ta shafe shekaru tana fama da karancin abinci, asarar da manoma ke tabkawa bayan sun yi girbi da kuma matsalar rashin aikin yi a tsanakin ‘yan kasar.

 

Har ila yau, aikin zai kuma samar da damar fitar da amfanin gona zuwa ketare, wanda hakan zai samar wa da Nijeriya biloyin Nairori.

 

Ta hanyar aikin na SAPZ, Nijeriya za ta iya samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, rage asarar da ake fuskanta duk shekara, bayan girbe amfanin gona da kudinsu ya kai kimanin Naira tiriliyan 3.5, samar da ingantacce wajen adana amfanin gona, samar da cibiyoyin bayar da horo ga manoma da kuma cike gibin da ake da shi a kasuwannin kasar.

 

Kashi na farko na aikin, an kaddamar da shi ne, a 2022, ta hanyar ware dala miliyan 538, wanda kuma za a wanzar da shi a cikin akalla sama da shekaru biyar.

 

Aikin na Bankin AfDB, zai samar da dala miliyan 210, inda kuma Bankin IsDB da IFAD, za su samar da dala miliyan 310, sai kuma gwamnatin tarayya da za ta samar da dala miliyan 18.05.

 

Jihohin Da Za Su Amfana Da Aikin:

Jihon da za su amfana da aikin su ne; Kaduna, Kano, Kwara, Kuros Riba, Imo, Ogun, Oyo, sai kuma Abuja.

 

A yanzu dai, Shugaban Bankin AfDB, Akinwunmi Adesina da kuma Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ne, ke jagorantar aikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Next Post

Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

17 hours ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Noma

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.