• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

by Abubakar Abba
4 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shirin inganta noma na musamman (SAPZ), an kirkiro shi ne, domin habaka fannin aikin noma a wasu jihohin kasar nan da aka zabo.

 

An ware wa aikin biliyoyin Nairori, wanda zai samar da riba mai dimbin yawa ga fannin na aikin noma.

  • 2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed
  • Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

Aikin ya samu goyon bayan Bankin Bunkasa Aikin Noma a Afirka (AfDB), Gidauniyar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa da Kasa (IFAD), Bankin Raya Addinin Muslunci (ISDB).

 

Labarai Masu Nasaba

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

Kazalika, a cikin daukacin gwamnatin tarayya da kuma na jihohin kasar, an tsara yadda za su dakile kalubalen da fannin aikin noma da kuma yadda za a sama wa manoman kasar sauki, bunkasa rayuwar mazauna karkara da kuma habaka tattalin arzikin kasar.

 

Akasarin manufar aikin na SAPZ shi ne, domin inganta aikin noma a karkara, maimakon fitar da amfanin gona kamar irin su Rogo, Shinkafa, Tumatir da kuma Koko zuwa birane ko kuma kasar waje, za a tanadar da kayan aiki a yankunan da aka tsara za su amfana da shirin, domin manoman yankin su samu ribar da ta kamata.

 

Daya daga cikin manyan matsalolin da ake samu a Nijeriya ita ce, gibin da ake samu a bangaren aikin noma domin samun riba.

 

Amma a wadannan yankunan da za a gudanar da aikin, za a samar da masana’antun sarrafa amfanin gona, kayan adana amfanin gona, wutar lantarki mai dorewa, tituna da kuma cibiyoyin bayar da horo.

 

Nijeriya dai, ta shafe shekaru tana fama da karancin abinci, asarar da manoma ke tabkawa bayan sun yi girbi da kuma matsalar rashin aikin yi a tsanakin ‘yan kasar.

 

Har ila yau, aikin zai kuma samar da damar fitar da amfanin gona zuwa ketare, wanda hakan zai samar wa da Nijeriya biloyin Nairori.

 

Ta hanyar aikin na SAPZ, Nijeriya za ta iya samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, rage asarar da ake fuskanta duk shekara, bayan girbe amfanin gona da kudinsu ya kai kimanin Naira tiriliyan 3.5, samar da ingantacce wajen adana amfanin gona, samar da cibiyoyin bayar da horo ga manoma da kuma cike gibin da ake da shi a kasuwannin kasar.

 

Kashi na farko na aikin, an kaddamar da shi ne, a 2022, ta hanyar ware dala miliyan 538, wanda kuma za a wanzar da shi a cikin akalla sama da shekaru biyar.

 

Aikin na Bankin AfDB, zai samar da dala miliyan 210, inda kuma Bankin IsDB da IFAD, za su samar da dala miliyan 310, sai kuma gwamnatin tarayya da za ta samar da dala miliyan 18.05.

 

Jihohin Da Za Su Amfana Da Aikin:

Jihon da za su amfana da aikin su ne; Kaduna, Kano, Kwara, Kuros Riba, Imo, Ogun, Oyo, sai kuma Abuja.

 

A yanzu dai, Shugaban Bankin AfDB, Akinwunmi Adesina da kuma Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ne, ke jagorantar aikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Next Post

Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

Related

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

6 days ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

6 days ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 weeks ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

3 weeks ago
Next Post
Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.