• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Mun Cafke ‘Yan Kwaya 50,901 Da Gurfanar Da 9,034 A Shekara 3 – Marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Mohamed Buba Marwa ya bayyana cewa sun samu nasarar cafke ‘yan kwaya guda 50,901 da suka kasance masu aikata laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi tare da samu nasarar gurfanarwa da daure mutum 9,034 hadi da kamo sama da tan-tan 7,561 na haramtattun kwayoyi a cikin watanni 38 da suka wuce.

A cikin shekaru uku kuma, hukumar ta lalata da tarwatsa hekta 1,057.33348 na tabar wiwi a sassa daban-daban na Nijeriya a wani mataki na nuna aikin ba sani ba sabo kan yaki da miyagun kwayoyi da safararsu.

  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci
  • Nijeriya Da Jamhoriyyar Benin Za Su Hada Kai Don Inganta Harkokin Kasuwanci

Sannan a cewarsa, wannan wani kyakkyawar sako ne ga masu mu’amala da miyagun kwayoyi da su gane cewa Nijeriya a yanzu ba za ta lamunci munanan ayyukansu ba.

Marwa ya shaida haka ne a ranar Litinin a Legas yayin da ke jawabi wajen kaddamar da mika ofishin da Gwamnatin Burtaniya ta gina domin agaza wa kokarin hukumar NDLEA na cigaba da yaki da masu mu’amala da miyagun kwayoyi da dakile safaran miyagun kwayoyi a Nijeriya.

A cewarsa, “Mun hadu a nan ne ba kawai domin mu kaddamar da sabon ginin ofishi ba, har ma da mu yi murna kan irin nasarorin da muka cimma kan yaki da muke yi da masu ta’anmuli da miyagun kwayoyi da safararsa. A yau, da wannan kaddamar da sabon ofishin da gwamnatin Burtaniya ta yi da nufin karfafa wa kokarinmu wajen ci gaba da dakile amfani da miyagun kwayoyi.

“Dole ne na jinjina da mika godiyarmu ga gwamnatin Burtaniya bisa wannan gagarumin gudunmawa da ta mana. Kuma, da kyakkyawar hadin guiwa da ke tsakani za mu samu nasarar ci gaba da dakile ayyukan ‘yan ta’adda da tsarkake Nijeriya daga ta’anmuli da miyagun kwayoyi hadi da jigilarsu.

“Wannan ofishin aikin ba kawai an gina domin gudanar da aiki zalla ba ne, zai kuma kyautata dangantaka a tsakanin kasashen biyu wajen ci gaba da yaki da safaran miyagun kwayoyi.”

A cewarsa, alfanun da sabon ofishin zai musu na da matukar yawa da suka hada da bincike, bibiya da kuma sanya ido kan miyagun kwayoyi da ake jigilarsu domin dakile aniyar masu mu’amala da su.

“Mun kama kilogiram 7,560,748.5 (Tan 7,561), ba kawai dakile miyagun kwayoyi ba ne har ma da toshe wa masu jigilar aniyarsu na rabawa a inda suke son rarrabawa. Mun kuma samu nasarar tarwatsa hekta 1,057.33348 na gonar tabar wiwi a cikin shekaru uku da suka wuce,” ya shaida.

Duk da kyautar ofishin, shugaban hukumar ya kuma sake neman hadin guiwar gwamnatin Burtaniya domin kara kyautata himma wajen yaki da matsalar sha da fataucin miyagun kwayoyi a tsakanin kasashen biyu.

A cewarsa, ba za su bari a yi sako-sako da wadanan nasarorin da suke samu ba, ya nemi jami’ansa da su kara himma wajen shiga lungu da sako domin dakile aniyar masu sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Da yake jawabinsa a wajen taron, mataimakin wakilin Burtaniya a Nijeriya, Jonny Badter, ya ba da tabbacin gwamnatin kasarsu na ci gaba da taimaka wa NDLEA da Nijeriya a bangarorin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da sauran muhimman bangarori.

Ya kuma nuna farin cikin gwamnatin Burtaniya kan yadda NDLEA ke samun gagarumin nasara wajen yaki da masu sha da masu fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya, ya ce kofarsu a bude take wajen ci gaba da taimaka wa Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawaitar Lalacewar Babbar Tashar Lantarki Ta Addabi ‘Yan Nijeriya

Next Post

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

2 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

4 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

4 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

8 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Next Post
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.