• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Muka Yi Musu A Shekara 7 –Shugaba Buhari

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Muna Kan Kokarin Magance Matsalar Hauhawar Farashin Kayan Masarufi —Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da auna kwazon ma’aikatun gwamnatinsa na kasarshe, inda ya bayyana cewa sun kaddamar da manyan ayyuka a sassa daban-daban na kasar nan domin cika wa ‘yan Nijeriya alkawarin da suka yi musu.
Da yake magana kan sake shirya kwatanta kwazon da gwamnatinsa ta samu, shugaban kasa ya lissafo wasu daga cikin nasarorin da ya samu a bangaren gona da tattalin arziki da lafiya da yakar cin hanci da rashawa da dai sauransu.

Shugaban kasa ya shaida wa mahalarta taron ciki har da tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta cewa sama da hanyoyi da suka kai kimanin kimomita 3,800 ya gina a fadin kasar nan, yayin da aka saya wa rundunar sojojin saman Nijeriya jiragen yaki har guda 38 domin fatattakar masu ‘yan ta’adda.

  • Mu Nemi Yafiyar ‘Yan Nijeriya Don Ba Lallai Mun Biya Musu Bukatunsu Ba – Aisha Buhari

Ya kara da cewa ‘yan Nijeriya miliyan 38.7 sun samu nasarar yin allurer rigakafin Korona, wanda ya sa aka samu kashi 35 na yawan ‘yan Nijeriya da suka yi rigakafin cutar.
A bangren kayayyakin more rayuwa kuwa, shugaban kasan ya ce gwamnatinsa ta samar da muhimman ayyukan ci gaban kasa da farfado da tattalin arziki wanda ta bar kyakkyawar tarihi.

Ya ce, “Wasu daga cikin nasarorin da muka samu sun hada da kammala hanyar Itakpe zuwa Ajaokuta ta nufi Warri mai nisan kimomita 326 da titin dogo da ke tsakanin Lagas zuwa Ibadan mai nisan sama da kimomita 156.5 da kuma kammala babban aikin tashar jirgin ruwa da ke Apapa a Jihar Legas.

“A bangren ayyukan hanya kuwa, wannan gwamnatin ta shiffida hanyoyi da suka kai kimomita 408 da gyara hanyoyin da suka kai kilomita 15,961 a dukkan sassa daban-daban da ke kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

“Manyan ayyukan hanyoyi da aka gina sun hada da gadar Neja mai tsawon kilomita 1.9 da ta hade jihohin Anambra da Delta, sannan an gyara hanyar Legas zuwa Shagamu ta nufi Ibadan mai hannu biyu da kuma ta Abuja zuwa Kaduna ta nufi Zariya har ta kai Kano da dai sauransu.

A cewasa, gwamnatin tarayya a karkashinsa ta yi namijin kokari wajen samar da ayyukan ci gaban kasa a shekarun bakwan da ta shafe a kan karagar mulki. Buhari ya ce gwamnatin tarayya ta gina hanyoyin tarayya har guda 21 wanda suka kasance jimillar nisansu ya kai kimomita 1,804.6.

Shugaban kasa ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ta yi kokari wajen bunkasa harkokin sufuri a filayen jiragen saman da ke fadin Nijeriya. Ya kara da cewa gwamnatinsa ta farfado da tattalin arziki wanda a baya ya samu koma-baya a wata ukun shekarar 2020.

A bangaren harkokin man fetur kuwa, shugaban kasa ya tunatar da cewa a ranar 16 ga watan Agustan 2021 ya rattaba hannu kan kudirin dokar man fetur wanda ya zama doka tare da samar da sauyi wajen kulawa da kamfanin mai na kasa. Ya ce dokar ya samar da kyakkyawan tsari da ya bunkasa kamfanin mai na kasa wajen kulawa da harkokin man Nijeriya.

A fannin karfafa tsaron kasa kuwa, shugaban kasa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi kokarin samar da makamai na zamani da wasu muhimman kayayyakin sojoji tare da ba su horo wajen tunkarar ‘yan ta’adda. Ya ce gwamnatinsa ta samu nasarar kara yawan ‘yansanda ta hanyar daukar sababbin jami’ai har guda 20,000 a tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021.

Bangaren yaki da cin hanci da rashawa kuwa, Buhari ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bankadowa tare da gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu.

Haka kuma a bangaren shirye-shiryen bunkasa zamantakewa kuwa, shugaban kasa ya ce, ana ciyar da daliban makaranta guda 9,990,862 a karkashin wannan shiri tare da daukar masu dafa aminci aiki har guda 128,531.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Da AMCON Sun Saka Bankin Polaris A Kasuwa

Next Post

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

7 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

10 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

12 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

15 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

15 hours ago
Next Post
2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.