ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Muka Yi Musu A Shekara 7 –Shugaba Buhari

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Nijeriya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da auna kwazon ma’aikatun gwamnatinsa na kasarshe, inda ya bayyana cewa sun kaddamar da manyan ayyuka a sassa daban-daban na kasar nan domin cika wa ‘yan Nijeriya alkawarin da suka yi musu.
Da yake magana kan sake shirya kwatanta kwazon da gwamnatinsa ta samu, shugaban kasa ya lissafo wasu daga cikin nasarorin da ya samu a bangaren gona da tattalin arziki da lafiya da yakar cin hanci da rashawa da dai sauransu.

Shugaban kasa ya shaida wa mahalarta taron ciki har da tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta cewa sama da hanyoyi da suka kai kimanin kimomita 3,800 ya gina a fadin kasar nan, yayin da aka saya wa rundunar sojojin saman Nijeriya jiragen yaki har guda 38 domin fatattakar masu ‘yan ta’adda.

  • Mu Nemi Yafiyar ‘Yan Nijeriya Don Ba Lallai Mun Biya Musu Bukatunsu Ba – Aisha Buhari

Ya kara da cewa ‘yan Nijeriya miliyan 38.7 sun samu nasarar yin allurer rigakafin Korona, wanda ya sa aka samu kashi 35 na yawan ‘yan Nijeriya da suka yi rigakafin cutar.
A bangren kayayyakin more rayuwa kuwa, shugaban kasan ya ce gwamnatinsa ta samar da muhimman ayyukan ci gaban kasa da farfado da tattalin arziki wanda ta bar kyakkyawar tarihi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Wasu daga cikin nasarorin da muka samu sun hada da kammala hanyar Itakpe zuwa Ajaokuta ta nufi Warri mai nisan kimomita 326 da titin dogo da ke tsakanin Lagas zuwa Ibadan mai nisan sama da kimomita 156.5 da kuma kammala babban aikin tashar jirgin ruwa da ke Apapa a Jihar Legas.

“A bangren ayyukan hanya kuwa, wannan gwamnatin ta shiffida hanyoyi da suka kai kimomita 408 da gyara hanyoyin da suka kai kilomita 15,961 a dukkan sassa daban-daban da ke kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

“Manyan ayyukan hanyoyi da aka gina sun hada da gadar Neja mai tsawon kilomita 1.9 da ta hade jihohin Anambra da Delta, sannan an gyara hanyar Legas zuwa Shagamu ta nufi Ibadan mai hannu biyu da kuma ta Abuja zuwa Kaduna ta nufi Zariya har ta kai Kano da dai sauransu.

A cewasa, gwamnatin tarayya a karkashinsa ta yi namijin kokari wajen samar da ayyukan ci gaban kasa a shekarun bakwan da ta shafe a kan karagar mulki. Buhari ya ce gwamnatin tarayya ta gina hanyoyin tarayya har guda 21 wanda suka kasance jimillar nisansu ya kai kimomita 1,804.6.

Shugaban kasa ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ta yi kokari wajen bunkasa harkokin sufuri a filayen jiragen saman da ke fadin Nijeriya. Ya kara da cewa gwamnatinsa ta farfado da tattalin arziki wanda a baya ya samu koma-baya a wata ukun shekarar 2020.

A bangaren harkokin man fetur kuwa, shugaban kasa ya tunatar da cewa a ranar 16 ga watan Agustan 2021 ya rattaba hannu kan kudirin dokar man fetur wanda ya zama doka tare da samar da sauyi wajen kulawa da kamfanin mai na kasa. Ya ce dokar ya samar da kyakkyawan tsari da ya bunkasa kamfanin mai na kasa wajen kulawa da harkokin man Nijeriya.

A fannin karfafa tsaron kasa kuwa, shugaban kasa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi kokarin samar da makamai na zamani da wasu muhimman kayayyakin sojoji tare da ba su horo wajen tunkarar ‘yan ta’adda. Ya ce gwamnatinsa ta samu nasarar kara yawan ‘yansanda ta hanyar daukar sababbin jami’ai har guda 20,000 a tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021.

Bangaren yaki da cin hanci da rashawa kuwa, Buhari ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bankadowa tare da gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu.

Haka kuma a bangaren shirye-shiryen bunkasa zamantakewa kuwa, shugaban kasa ya ce, ana ciyar da daliban makaranta guda 9,990,862 a karkashin wannan shiri tare da daukar masu dafa aminci aiki har guda 128,531.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.