ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Muka Yi Musu A Shekara 7 –Shugaba Buhari

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Nijeriya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da auna kwazon ma’aikatun gwamnatinsa na kasarshe, inda ya bayyana cewa sun kaddamar da manyan ayyuka a sassa daban-daban na kasar nan domin cika wa ‘yan Nijeriya alkawarin da suka yi musu.
Da yake magana kan sake shirya kwatanta kwazon da gwamnatinsa ta samu, shugaban kasa ya lissafo wasu daga cikin nasarorin da ya samu a bangaren gona da tattalin arziki da lafiya da yakar cin hanci da rashawa da dai sauransu.

Shugaban kasa ya shaida wa mahalarta taron ciki har da tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta cewa sama da hanyoyi da suka kai kimanin kimomita 3,800 ya gina a fadin kasar nan, yayin da aka saya wa rundunar sojojin saman Nijeriya jiragen yaki har guda 38 domin fatattakar masu ‘yan ta’adda.

  • Mu Nemi Yafiyar ‘Yan Nijeriya Don Ba Lallai Mun Biya Musu Bukatunsu Ba – Aisha Buhari

Ya kara da cewa ‘yan Nijeriya miliyan 38.7 sun samu nasarar yin allurer rigakafin Korona, wanda ya sa aka samu kashi 35 na yawan ‘yan Nijeriya da suka yi rigakafin cutar.
A bangren kayayyakin more rayuwa kuwa, shugaban kasan ya ce gwamnatinsa ta samar da muhimman ayyukan ci gaban kasa da farfado da tattalin arziki wanda ta bar kyakkyawar tarihi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Wasu daga cikin nasarorin da muka samu sun hada da kammala hanyar Itakpe zuwa Ajaokuta ta nufi Warri mai nisan kimomita 326 da titin dogo da ke tsakanin Lagas zuwa Ibadan mai nisan sama da kimomita 156.5 da kuma kammala babban aikin tashar jirgin ruwa da ke Apapa a Jihar Legas.

“A bangren ayyukan hanya kuwa, wannan gwamnatin ta shiffida hanyoyi da suka kai kimomita 408 da gyara hanyoyin da suka kai kilomita 15,961 a dukkan sassa daban-daban da ke kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

“Manyan ayyukan hanyoyi da aka gina sun hada da gadar Neja mai tsawon kilomita 1.9 da ta hade jihohin Anambra da Delta, sannan an gyara hanyar Legas zuwa Shagamu ta nufi Ibadan mai hannu biyu da kuma ta Abuja zuwa Kaduna ta nufi Zariya har ta kai Kano da dai sauransu.

A cewasa, gwamnatin tarayya a karkashinsa ta yi namijin kokari wajen samar da ayyukan ci gaban kasa a shekarun bakwan da ta shafe a kan karagar mulki. Buhari ya ce gwamnatin tarayya ta gina hanyoyin tarayya har guda 21 wanda suka kasance jimillar nisansu ya kai kimomita 1,804.6.

Shugaban kasa ya tabbatar da cewa gwamnatinsa ta yi kokari wajen bunkasa harkokin sufuri a filayen jiragen saman da ke fadin Nijeriya. Ya kara da cewa gwamnatinsa ta farfado da tattalin arziki wanda a baya ya samu koma-baya a wata ukun shekarar 2020.

A bangaren harkokin man fetur kuwa, shugaban kasa ya tunatar da cewa a ranar 16 ga watan Agustan 2021 ya rattaba hannu kan kudirin dokar man fetur wanda ya zama doka tare da samar da sauyi wajen kulawa da kamfanin mai na kasa. Ya ce dokar ya samar da kyakkyawan tsari da ya bunkasa kamfanin mai na kasa wajen kulawa da harkokin man Nijeriya.

A fannin karfafa tsaron kasa kuwa, shugaban kasa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi kokarin samar da makamai na zamani da wasu muhimman kayayyakin sojoji tare da ba su horo wajen tunkarar ‘yan ta’adda. Ya ce gwamnatinsa ta samu nasarar kara yawan ‘yansanda ta hanyar daukar sababbin jami’ai har guda 20,000 a tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021.

Bangaren yaki da cin hanci da rashawa kuwa, Buhari ya sha alwashin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bankadowa tare da gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu.

Haka kuma a bangaren shirye-shiryen bunkasa zamantakewa kuwa, shugaban kasa ya ce, ana ciyar da daliban makaranta guda 9,990,862 a karkashin wannan shiri tare da daukar masu dafa aminci aiki har guda 128,531.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.