ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Namadi Sambo Ya Gwangwaje Atiku Da Kyautar Ofishin Yakin Neman Zabe A Kaduna

by Muhammad
4 years ago

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya kaddamar da sabon ofishinsa na shiyyar Arewa maso Yamma.

Ofishin yakin neman zaben a Jihar Kaduna, wanda tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo ya bayar a matsayin gudumawa.

  • Atiku Ya Tafi Turai Kan Harkar Kasuwanci 
  • Atiku Ya Yi Alkawarin Dawo Da Zaman Lafiya Da Sake Farfado Da Masana’antu A Jihar Kaduna

A wajen kaddamar da bude ofishin, jam’iyyar PDP ta yabawa tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, bisa bayar da gudunmuwar ofishin yakin neman zaben jam’iyyar domin samun nasarar jam’iyyar a zaben 2023.

ADVERTISEMENT

Atiku ya shaida wa magoya bayan jam’iyyar da suka taru a wajen bikin kaddamar da ofishin da su yi wa jam’iyyar aiki tukuru domin ganin ta samu nasara a zaben.

A cewarsa, duk wanda ya yi wa jam’iyyar aiki za a ba shi kyauta mai kyau bayan an kammala zabe.

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

Ya ce, “Ina son in yaba wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, bisa irin wannan karamci da ya yi wajen bayar da wannan ofishin, kowa ya yi kokari wajen ganin jam’iyyarmu ta samu nasara a zabe mai zuwa kuma ta yi nasara sosai, a wannan karon na ga hadin kan da aka samu a cikin jam’iyyar da jajircewar ‘ya’yan jam’iyyar na jihar Kaduna na kishin ganin mun yi nasarar a jihar da zaben ‘yan majalisun tarayya da na shugaban kasa.

“Ina tabbatar muku cewa jam’iyya a matakin kasa za ta ba ku goyon baya da kuma tabbatar da nasara a jiha a kowane mataki, idan kun yi wa jam’iyyar aiki da kyau kuma kuka yi wa Atiku aiki da kyau kuma ya ci zaben shugaban kasa, za a ba ku kyauta mai tsoka. .”

Tsohon mataimakin shugaban kasa Sambo, wanda ya yi magana tun farko, ya ce ‘ya’yan jam’iyyar a jihar Kaduna a shirye suke su ba Atiku gudunmawa a jihar.

Ya ce sabon ofishin da aka bayar zai zama ofishin jam’iyyar a shiyyar Arewa maso Yamma da kuma jihar.

“Jihar Kaduna a shirye ta ke ta zabi PDP a zabe mai zuwa a 2023, mun riga mun yi aiki don ganin nasararku da jam’iyya a zabe mai zuwa.

“Babu shakka za mu yi nasara a wannan zabe domin kowa za a yi aiki tare domin samun nasara,” inji Sambo.

Har ila yau, a wajen taron, Amb Usman Elkudan, daya daga cikin makusantan tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo, ya ce wannan mafarin ne na goyon bayan da maigidansa ya yi wa takarar Atiku Abubakar.

Ya yi alkawarin za su ci zabe a kowane mataki.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
Siyasa

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
Siyasa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Next Post
Hu Hailan: Masaniyar Kasar Sin Da Ta Kai Matsayin Koli A Fannin Kimiyyar Kwakwalwa Da Jijiyoyi A Duniya

Hu Hailan: Masaniyar Kasar Sin Da Ta Kai Matsayin Koli A Fannin Kimiyyar Kwakwalwa Da Jijiyoyi A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.